| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
ASUU: Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Nijeriya ta shiga yajin aikin gargaɗi
Shugaban ƙungiyar Farfesa Chris Piwuna ne ya sanar da hakan a lokacin wani taron manema labarai da aka gudanar a Jami’ar Abuja, a ranar Lahadi.
ASUU: Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Nijeriya ta shiga yajin aikin gargaɗi
An shafe shekaru da dama ana samun matsala tsakanin gwamnatin tarayya da malaman na jami'o'i
12 Oktoba 2025

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya ASUU a ranar Lahadi ta sanar da shiga yajin aiki na makonni biyu, wanda zai kasance cikakke kuma gaba ɗaya, a duka jami’o’in gwamnati na ƙasar.

Shugaban ƙungiyar Farfesa Chris Piwuna ne ya sanar da hakan a lokacin wani taron manema labarai da aka gudanar a Jami’ar Abuja, a ranar Lahadi.

 “’Yan jarida abokan aikinmu, babu wani abu mai ƙarfi a yanzu da zai hana aiwatar da matsayar kwamitin zartarwa na ASUU ta shiga yajin aikin gargaɗi na makonni biyu bayan ƙarewar wa’adin kwanaki 14 da aka bayar tun ranar 28 ga Satumban, 2025.

“Saboda haka, duka rassan ASUU an umurce su da su dakatar da ayyukansu daga misalin ƙarfe 12 na daren Litinin, 13 ga Oktoban, 2025.

“Yajin aikin gargadin zai kasance cikakke kuma gaba ɗaya, kamar yadda aka amince a taron NEC na ƙarshe,” kamar yadda Piwuna ya bayyana.

Sabuwar taƙaddama tsakanin malaman jami’a da gwamnatin tarayya na zuwa ne duk da ƙoƙarin tattaunawa don kauce wa wani sabon yajin aiki a jami’o’in ƙasar.

A ranar Laraba, Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana a Abuja cewa gwamnati ta shiga matakin ƙarshe na tattaunawa da ASUU da sauran ƙungiyoyi domin warware matsalolin da suka shafi albashi, kuɗaɗen tallafi, da aiwatar da yarjejeniyar ASUU ta shekarar 2009.

Rumbun Labarai
Za mu bai wa kowane jami'in soja da ke bakin aikinsa kariya  - Ministan Tsaron Nijeriya
An kama hodar ibilis mai nauyin kilogiram 1,000 a Nijeriya
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura