| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Sojojin Nijeriya sun kama 'yan ta'adda 450, sun kuɓutar da mutum 180 a Satumba - Hedkwatar Tsaro
Kazalika mai magana da yawun hedkwatar tsaron Nijeriya Manjo Janar Markus Kangye, ya ce dakarunsu sun ƙwato tarin manyan makamai da sauran kayan aiki na 'yan ta'adda.
Sojojin Nijeriya sun kama 'yan ta'adda 450, sun kuɓutar da mutum 180 a Satumba - Hedkwatar Tsaro
Hedkwatar Tsaron Nijeriya ta ce dakarunta sun aiwatar da waɗannan ayyuka ne a watan Satumban da ya gabata
5 Oktoba 2025

Hedkwatar Tsaron Nijeriya ta ce dakarunta da ke aikin wanzar da tsaro a sassa daban-daban na ƙasar sun kama ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga aƙalla 450 a watan Satumba.

Ta bayyana haka ne a wata sanarwa da mai magana da yawunta Manjo Janar Markus Kangye ya fitar ranar Asabar a Abuja, babban birnin ƙasar.

Manjo Janar Kangye ya ƙara da cewa dakarun nasu sun kuɓutar da mutum fiye da 180 daga hannun masu garkuwa da mutane, yana mai cewa ‘yan ta’adda aƙalla 39 sun yi saranda yayin samamen da aka kai musu.

“A watan Satumba na shekarar 2025, dakarunmu sun kuɓutar da fararen-hula 180 da aka yi garkuwa da su, sun kama ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga 450, sannan sun kawar da masu aikata laifuka da dama a samame daban-daban da rundunoninmu suka kai,” in ji Manjo Janar Kangye.

Wuraren da ‘yan ta’adda suke da ƙarfi

Mai magana da yawun hedkwatar tsaron ta Nijeriya ya ce dakarunsu sun ƙama ƙaimi wajen kai samame a wuraren da ‘yan ta’adda suke da ƙarfi a jihohin Borno, Adamawa, da Yobe daga ranar 23 zuwa 30 ga watan Satumba.

“Dakarunmu sun kai samame a ƙananan hukumomin Konduga, Gwoza, Mafa, Gubka, Monguno, Damboa, Biu, da Kukawa da ke JIhar Borno. Kazalika sun kai samame a ƙananan hukumomin Madagali, Hong, da Mubi South a Jihar Adamawa da kuma Gujba a Jihar Yobe,” a cewarsa.

Manjo Janar Kangye ya ƙara da cewa waɗannan samame sun kai ga lalata sansanonin ‘yan ta’adda da ƙwato manyan makamai da kuma kama masu haɗa baki da su.

Ya ce, :“Sojojinmu sun kawar da ‘yan ta’adda da dama tare da ƙwato makamai da alburusai da abubuwan fashewa, sannan suka lalata sansanoninsu. Kazalika mun kama mutum 21 da ke yi wa ‘yan ta’adda aiki wato infoma.”

Rumbun Labarai
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso