NIJERIYA
2 minti karatu
Geoffrey Nnaji: Ministan Kimiyya da Fasaha na Nijeriya ya yi murabus kan takardar digiri ta bogi
Hukumomi a Jami’ar UNN da ke Nsukka sun ce duk da cewa Geoffrey Nnaji ya fara karatu a jami’ar a shekarar 1981 amma bai kammala karatun digirinsa ba.
Geoffrey Nnaji: Ministan Kimiyya da Fasaha na Nijeriya ya yi murabus kan takardar digiri ta bogi
Geoffrey Uche Nnaji ya ajiye aiki ne bayan an zarge shi da amfani da takaradar digiri na boge
8 Oktoba 2025

Ministan Kimiyya da Fasaha na Nijeriya, Geoffrey Uche Nnaji, ya sauka daga muƙaminsa bayan rahotanni sun ce ya yi amfani da ta takardar shaidar digiri ta boge.

Wata sanarwar da mai bai wa shugaban Nijeriya shawara kan watsa labarai, Bayo Onanuga ya fitar ranar Talata, ta ce shugaban ya amshi takardar barin aikin ministan.

“Shugaba ya naɗa Nnaji a muƙamin minista ne a watan Agustan shekarar 2023. Ya ajiye aiki a yau a wata wasiƙa inda ya gode wa shugaban kan damar da ya ba shi ta yi wa Nijeriya hidima,” in ji sanawar.

“Nnaji ya ce abokan adawarsa na siyasa ne ke masa bi-ta-da ƙulli. Shugaba Tinubu ya gode masa kan hidimarsa kuma ya yi masa fatan aheri,” in ji Onanuga.

Matsalar da Nnaji ya fuskanta ta kunno kai ne bayan rahotanni sun ce ministan bai kammala karatun digiri ba a Jami’ar UNN ta Nsukka, wadda ya gabatar da takardar shaidar digirinta a lokacin tantance shi domin ba shi muƙamin minista.

Hukumomi a Jami’ar UNN da ke Nsukka sun ce duk da cewa Geoffrey Nnaji ya fara karatu a jami’ar a shekarar 1981 amma bai kammala karatun digirinsa ba.

Kazalika hukumar da ke kula da yi wa ƙasa hidima ta Nijeriya (NYSC) ta ce ministan bai yi wa ƙasar hidima ba, lamarin da ya sa aka ce takardar shaidar yi wa ƙasa hidimar da ya yi amfani da ita ma ta bogi ce.  

Rumbun Labarai
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka
Trump ya umarci Ma'aikatar Yaƙi ta Amurka ta soma shirin yiwuwar kai hari Nijeriya
Tinubu ya mayar da martani bayan Amurka ta ce ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Nijeriya
Gwamnatin Nijeriya ta sake jaddada aniyarta ta yaƙi da tsattsauran ra'ayi
Samaila Bagudo: 'Yan bindiga sun sace Mataimakin Kakakin Majalisar Jihar Kebbi
Donald Trump ya ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla
‘Yan sandan Nijeriya sun ceto ‘yan kasashen waje 23 da aka yi garkuwa da su
An yi gagarumin garambawul ga rundunar sojojin ƙasa ta Nijeriya
EFCC ta tilasta wa boka dawo da gidaje da motocin da ya damfari wani mutum a Nijeriya