| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
‘Yan Majalisar Wakilan Nijeriya sun soki kudirin Majalisar Amurka kan zargin kisan Kiristoci
‘Yan majalisar sun ce Nijeriya ba ta fuskantar rikicin addini, inda suka bayyana buƙatar ɗaukar matakin diflomasiyya.
‘Yan Majalisar Wakilan Nijeriya sun soki kudirin Majalisar Amurka kan zargin kisan Kiristoci
Nigerian House of Reps
8 Oktoba 2025

Majalisar wakilan Nijeriya ta yi watsi da kaulin da ke bayyana cewa Nijeriya na fuskantar ƙalubalen tsaro na addini ko wanda gwamnati ke daukar nauyi.

Wannan mataki ya zo ne a matsayin martani ga ƙudirin da aka gabatar a Majalisar Dokokin Amurka a ranar 11 ga Maris din 2025.

Ƙudurin na neman a ayyana Najeriya a matsayin “Kasar da ke da damuwa ta musamman” saboda zarge-zargen aikatawa, amincewa, shiryawa, da take hakkin ‘yancin yin addini.

Da take mayar da martani, Majalisar ta umarci hukumomin gwamnati da abin ya shafa, gami da Ma'aikatar Harkokin Waje, da su tattara da kuma isar da kwararan shaidun da suka saɓa da iƙirarin da aka yi a cikin kudirin na Amurka.

Matakin dai ya biyo bayan ƙudirin da mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Kalu ya gabatar na muhimmancin gaggawa ga jama’a, kuma ‘yan majalisar suka amince da shi baki ɗaya.

‘Yan majalisar sun yi korafin cewa Najeriya ba ta fuskantar rikicin addini ko kadan, inda suka jaddada bukatar gaggawa don daukar matakin diflomasiyya don ganin kudurin bai yi tasiri a majalisar dokokin Amurka ba.

Makonni biyu da suka gabata, Gwamnatin Tarayya ta yi watsi da ikirarin cewa ‘yan ta’adda a Najeriya na yi wa Kiristoci kisan kare-dangi, inda ta bayyana zargin a matsayin “ƙarya, mara tushe, abin kyama, da kuma raba kan jama’a.”

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Ministan Watsa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya ce bayyana kalubalen tsaro a Najeriya a matsayin yakin da ake yi da ƙungiyar addini guda, gaskiya babban kuskure ne.

“Irin wadannan ikirari ƙarya ce tsagwaron ta, marar tushe, abar kyama, da raba kan juna.”

Ministan ya bayyana cewa masu tsattsauran ra'ayi na kai hari kan 'yan Najeriya mabiya addinai daban-daban, inda ya kuma bayyana irin ci gaban da sojoji suka samu a yakin da ake yi da kungiyoyin 'yan ta'adda a kasar.

Rumbun Labarai
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka