NIJERIYA
1 minti karatu
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da shirin rigakafin ƙyanda da polio domin amfanar yara miliyan 16
Manufar wannan shiri ita ce a kawar da ciwon ƙyanda zuwa shekarar 2030, ta hanyar ƙarfafa rigakafin yara na yau da kullum, inganta bincike da sa ido kan ɓarkewar cuta, da kuma samar da shirye-shiryen kawar da ƙyanda a asibitoci na matakin farko.
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da shirin rigakafin ƙyanda da polio domin amfanar yara miliyan 16
An gudanar da wannan taron ne a ranar Litinin a ɗakin taro na Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, babban birnin ƙasar. / Nigerian Ministry of Health
6 Oktoba 2025

Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da shirin rigakafin cututtuka irin su ƙyanda da shan inna da ta kansar bakin mahaifa wato HPV, da kuma wasu cututtukan da ake watsi da su a faɗin ƙasar.

An gudanar da wannan taron ne a ranar Litinin a ɗakin taro na Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, babban birnin ƙasar.

Manufar wannan shiri ita ce a kawar da ciwon ƙyanda zuwa shekarar 2030, ta hanyar ƙarfafa rigakafin yara na yau da kullum, inganta bincike da sa ido kan ɓarkewar cuta, da kuma samar da shirye-shiryen kawar da ƙyanda a asibitoci na matakin farko da kuma amfani da sabbin fasahohi wajen gudanar da ayyuka.

Ana sa ran yara miliyan 16 za su karɓi allurar rigakafi a wannan kamfe, wanda ya ƙunshi yara masu shekaru daga tara zuwa goma sha huɗu da za a yi musu allurar rigakafin.