| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Sojojin Nijeriya sun kuɓutar da mutane 37 da aka yi garkuwa da su, sun kashe ‘yan ta’adda 9
Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa haɗakar sojojin ƙasa na Nijeriya da wasu dakarun ƙasar sun kashe ‘yan ta’adda tara, tare da kama mutum 8 da ake zargi da laifuka, da ƙwato manyan makamai.
Sojojin Nijeriya sun kuɓutar da mutane 37 da aka yi garkuwa da su, sun kashe ‘yan ta’adda 9
A wani samame daban a iyakar Ekiti da Kogi, sojojin bataliya ta 148 sun kashe ‘yan ta’adda biyu
9 Oktoba 2025

Sojojin Nijeriya sun kuɓutar da mutum 37 da aka yi garkuwa da su, a wani samame na musamman na yaƙi da ta’addanci da satar mutane a faɗin ƙasar tsakanin 2 zuwa 6 ga Oktoban 2025.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa haɗakar sojojin ƙasa na Nijeriya da wasu dakarun ƙasar sun kashe ‘yan ta’adda tara, tare da kama mutum 8 da ake zargi da laifuka, tare da ƙwato manyan makamai.

A yankin Arewa maso Gabas, sojojin bataliya ta 151 Task Force sun yi kwanton-ɓauna ga ‘yan ta’addan ISWAP da Boko Haram a kusa da garin Dipchari a Ƙaramar Hukumar Bama ta Jihar Borno, inda suka kashe ‘yan ta’addan biyar a abin da aka bayyana a matsayin “gagarumar musayar wuta.”

“A wani samame daban a iyakar Ekiti da Kogi, sojojin bataliya ta 148 sun kashe ‘yan ta’adda biyu, tare da ƙwato bindigogi biyu ƙirar AK-47.

“Haka kuma, bataliya ta 3 ta daƙile wani hari mai girma da aka kai mata, inda ta jikkata da dama daga cikin maharan inda ta kashe ɗaya daga cikinsu, yayin da sauran suka tsere da raunukan harbin bindiga.

 “A jihohi da dama ciki har da Borno, Katsina, Imo, da Filato, sojoji sun kama mutane takwas da ake zargi da hannu a ta’addanci, satar mutane, da safarar makamai.

“Cikin waɗanda aka kama akwai wani da ake zargi da kasancewa mai kai wa ISWAP kaya a Monguno, wani abokin hulɗar ‘yan ta’adda a Kukawa, wani jami’in ƙungiyar ‘yan a-ware IPOB/ESN a Imo da kuma wani mai safarar makamai a Jihar Filato.

“Sojoji sun kuma ƙwato makamai da dama ciki har da ƙaramar bindiga ƙirar gida, da harba-ruga ɗaya, kurtunu na AK-47 ɗauke da alburusai fiye da 100 iri daban-daban, da kuma babura da dama da ake zargin ana amfani da su wajen aikata laifuka.”

Rumbun Labarai
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka