| hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Trump, Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a birnin Sharm el-Sheikh a ranar Litinin
Masar ta bayyana cewa taron zaman lafiyar zai tattaro shugabannin ƙasashe fiye da 20 inda za a tattauna kan batun kawo ƙarshen yaƙin Gaza da ƙarfafa ƙoƙarin kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali a Gabas ta Tsakiya da wasu muhimman abubuwa.
Trump, Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a birnin Sharm el-Sheikh a ranar Litinin
Za a gudanar da taron a birnin Sharm el-Sheikh na Masar
12 Oktoba 2025

Masar za ta shirya wani ƙasa da ƙasa kan zaman lafiya na ƙasa da ƙasa a birnin Sharm el-Sheikh da ke bakin Tekun Maliya a ranar Litinin, wanda Shugaba Abdel Fattah el-Sisi da takwaransa na Amurka, Donald Trump, za su jagoranta.

Wata sanarwa daga fadar shugaban kasa a daren Asabar ta bayyana cewa taron zai tattaro shugabanni daga ƙasashe fiye da 20.

Manufar taron ita ce “kawo ƙarshen yaƙin Gaza, ƙarfafa ƙoƙarin kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali a Gabas ta Tsakiya, da kuma fara wani sabon mataki na tsaro da kwanciyar hankali a yankin,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa wannan taron “yana zuwa ne bisa hangen nesa na Shugaban Amurka Trump na samar da zaman lafiya a yankin da kuma ƙoƙarinsa na kawo ƙarshen rikice-rikice a duniya.”

A ranar Laraba Trump ya sanar da cewa Isra’ila da Hamas sun amince da mataki na farko na wani shiri mai matakai 20 da ya gabatar a ranar 29 ga Satumba don cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da sakin dukkan fursunonin Isra’ila da ke hannun Hamas a musayar fursunoni Falasdinawa kusan 2,000, da kuma janye sojojin Isra’ila daga dukkan yankin Gaza.

Mataki na farko na wannan yarjejeniya ya fara aiki da ƙarfe 12 na rana agogon cikin gida (0900 GMT) a ranar Juma’a.

Mataki na biyu na shirin ya ƙunshi kafa sabon tsarin mulki a Gaza, samar da wata rundunar tsaro da za ta ƙunshi Falasɗinawa da sojoji daga ƙasashen Larabawa da Musulmi, da kuma ƙwace makamai daga hannun Hamas.

Tun daga watan Oktoba na 2023, hare-haren Isra’ila sun kashe Falasɗinawa fiye da 67,600 a Gaza, yawancinsu mata da yara, tare da mayar da yankin kufai da ba ya zaunuwa.

Rumbun Labarai
Bayanai na hukuma sun nuna cewa sojojin Isra'ila sun yi yunkurin kashe kansu sau 279 cikin wata 18
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta
Wani bidiyo ya nuna yadda Isra'ila ke cin zarafin fursunonin Falasɗinawa gabanin sakin su
Sojojin Amurka sun isa Isra'ila domin sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Sojojin Isra'ila sun fara janyewa a hankali zuwa gabashin Gaza: Kafofin watsa labarai
Gwamnatin Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta Trump
Shekaru biyu na kisan kiyashin Isra'ila a Gaza: Falasdinawa suna shan yunwa da cin-amana