| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Gwamnatin jihar Kogi a Nijeriya ta yi alhinin mutuwar mutum 26 a hatsarin kwale-kwale
Hatsarin kwale-kwale ya zama ruwan dare a Nijeriya, inda ake yawan samun asarar rayuka saboda hakan, musamman a yankunan da ke bakin koguna.
Gwamnatin jihar Kogi a Nijeriya ta yi alhinin mutuwar mutum 26 a hatsarin kwale-kwale
Hatsarin kwale-kwale a Jihar Kogi
1 Oktoba 2025

Gwamnatin jihar Kogi ta bayyana matuƙar alhininta kan mummunan hatsarin kwale-kwale da ya faru a kan Kogin Neja, inda aƙalla mutum 26 suka rasa rayukansu.

Sanarwar da Kwamishinan Yada Labarai da Sadarwa na jihar, Kingsley Femi Fanwo ya fitar a ranar Laraba ta ce wannan mummunan lamari ya rutsa da ‘yan kasuwa da suka taso daga ƙaramar hukumar Ibaji ta jihar Kogi zuwa kasuwar Ilushi a jihar Edo.

Gwamna Ahmed Usman Ododo ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, ya kuma umurci hukumomin da abin ya shafa ciki har da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jiha da su haɗa kai da ƙananan hukumomin yankin, wajen bayar da tallafi da kuma agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa.

Gwamna Ododo ya ƙara da ba da tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta ƙara ƙaimi tare da hadin-gwiwa da hukumomin tarayya na inganta matakan tsaro a magudanan ruwa domin hana sake afkuwar irin wannan bala’i.

Ya yi kira ga jama’a a yankunan da ke gaɓar kogi da su ba da fifikon tsaro a ko da yaushe ta hanyar guje wa wuce gona da iri, da kuma amfani da rigar kariya da sauran matakan kariya a duk lokacin da suke tafiya ta ruwa.

Hatsarin kwale-kwale ya zama ruwan dare a Nijeriya, inda ake yawan samun asarar rayuka saboda hakan, musamman a yankunan da ke bakin koguna.

Rumbun Labarai
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso