AFIRKA
2 minti karatu
Dakarun RSF a Sudan sun sake kai hari filin jirgin saman Khartoum a rana ta uku a jere
Jiragen sama marasa matuƙa na RSF sun sake kai wa filin jirgin sama na Khartoum hari, yayin da majiyoyin tsaron Sudan suka tabbatar da cewa babu wata ɓarna da aka samu a wurin.
Dakarun RSF a Sudan sun sake kai hari filin jirgin saman Khartoum a rana ta uku a jere
An ji ƙarar fashewar abubuwa a filin jirgin saman na Khartoum, a cewar kafar. / AP
15 awanni baya

Dakarun rundunar Rapid Support Forces (RSF) a ranar Alhamis sun kai wani sabon hari filin jirgin saman Khartoum na ƙasar Sudan da jiragen yaƙi marasa matuƙa a rana ta uku a jere.

Rahotanni sun bayyana cewa, jirage guda bakwai sun kai hare-hare a filin jirgin saman da kuma wasu unguwanni, lamarin da ya haifar da fargaba da tashin hankali, kamar yadda kafar yaɗa labarai ta Sudan ta rawaito.

An ji ƙarar fashewar abubuwa a filin jirgin, a cewar kafar.

Tun daga ranar Talata rundunar RSF ta ƙaddamar da hare-hare a filin jirgin da kuma wasu mahimman wurare a Jihar Khartoum, kwana guda kafin sake buɗe shi bayan shafe fiye da shekaru biyu a rufe.

A ranar Laraba ne aka samu jirgin farar-hula na fasinja karo na farko da ya sauka a filin jiragen saman.

Ba a samu ɓarna sosai a filin jirgin ba bayan harin na RSF, kamar yadda majiyoyin tsaro suka shaida wa jaridar Rakoba News.

A cewar jaridar, hare-haren baya bayan nan kan mahimman wurare na ƙasar na nuni da “yadda aka samu canji a yanayin rikicin" tsakanin dakarun RSF da sojojin Sudan, daga fafatawa ta ƙasa zuwa amfani da jirage marasa matuƙa a matsayin makamin soji da matsin lamba na siyasa.

Kawo yanzu dai babu wani ƙarin haske daga ƙungiyar 'yan tawayen kan waɗannan rahotannin.

Tun a watan Afrilun 2023 ne sojoji da dakarun RSF a Sudan suke gwabza yaƙi wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 20,000 tare da raba miliyan 14 da muhallansu, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya da hukumomin yankin.