| hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Gwamnatin Iran ta kashe babban wanda yake yi wa Isra'ila leƙen asiri
Mutumin shi ne "wanda ya fi yi wa Isra'ila leƙen asiri a ƙasar Iran," a cewar jaridar Mizan wadda fannin shari'a na Iran yake wallafawa.
Gwamnatin Iran ta kashe babban wanda yake yi wa Isra'ila leƙen asiri
Mutumin shi ne "wanda ya fi yi wa Isra'ila leƙen asiri a ƙasar Iran," a cewar jaridar Mizan wadda fannin shari'a na Iran yake wallafawa.
29 Satumba 2025

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan wani mutum mai suna Bahman Choobiasl, wanda aka yi zargin cewa shi ne wanda ya fi yi wa Isra’ila leƙen asiri a ƙasar, kamar yadda jaridar Mizan, wadda fannin shari’a na ƙasar ke wallafawa ta ruwaito.

Choobiasl ya yi aiki “a muhimman shirye-shirye na hanyoyin sadarwa“ kuma ya riƙa aika bayanai game da “hanyoyin shigo da kayan lataroni,” a cewar Mizan a ranar Litinin.

"Babban dalilin hukumar leƙen asirin Isra’ila ta Mossad na yin aiki da wanda aka hukunta shi ne na bayar da haɗin kai domin samun bayanan hukumomin gwamnati tare da yin kutse a rumbunan adana bayanai na hukumomin Iran, ciki har da hanyoyin shigo da kayan lataroni," in ji Mizan.

MDD ta sake ƙaƙaba wa Iran sabbin takunkumai bayan kasa cim ma matsaya a tattaunawar nukiliya

Kotun Ƙolin Iran ta yi watsi da ɗaukaka ƙarar da mutumin ya yi inda ta tabbatar da hukuncin kisa a kansa bisa laifin “cin hanci a duniya,” a cewar jaridar Mizan.

Ƙaruwar zartar da hukuncin kisa

Iran, wadda ta daɗe tana yaƙin-sunƙuru da Isra’ila, ta kwashe shekaru da dama tana zartar da hukuncin kisan kan mutanen da take zargi da yi wa hukumar leƙen asirin Isra’ila Mossada aiki.

A watan Yunin da ya gabata, rikici tsakanin Iran da Isra’ila ya yi ƙamari inda suka gwabza yaƙi kai-tsaye bayan Isra’ila ta kai hare-hare a wurare da dama a Iran, waɗanda ake gani ta yi su ne bayan samun bayanan sirri daga cikin ƙasar.

Adadin ‘yan ƙasar Iran da gwamnati ta kashe sakamakon yi wa Isra’ila aiki ya ƙaru sosai a wannan shekarar, inda bayanai suka nuna cewa a watannin baya bayan nan an kashe aƙalla mutum 10.

Rumbun Labarai
Sau 27 Yahudawa 'yan-kama-wuri-zauna suka kutsa Masallacin Kudus a watan da ya wuce - Falasdinu
Bayanai na hukuma sun nuna cewa sojojin Isra'ila sun yi yunkurin kashe kansu sau 279 cikin wata 18
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta
Wani bidiyo ya nuna yadda Isra'ila ke cin zarafin fursunonin Falasɗinawa gabanin sakin su
Trump, Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a birnin Sharm el-Sheikh a ranar Litinin
Sojojin Amurka sun isa Isra'ila domin sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Sojojin Isra'ila sun fara janyewa a hankali zuwa gabashin Gaza: Kafofin watsa labarai