| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Sojojin da suka yi juyin mulki a Madagascar sun ce a shirye suke su tattauna da Tarayyar Afirka
"Ba mu yi mamakin matakin da aka ɗauka ba. (Amma) daga yanzu, za mu yi tattaunawar sulhu ta bayan-fage. Za mu ga yadda za ta kaya," in ji Kanar Michael Randrianirina.
Sojojin da suka yi juyin mulki a Madagascar sun ce a shirye suke su tattauna da Tarayyar Afirka
Randrianirina ya ce zai sha rantsuwar kama aiki ranar Jumma'a a gaban kotun kundin tsarin mulki ta ƙasar
17 Oktoba 2025

Jagoran sojojin da suka yi juyin mulki a Madagascar, Kanar Michael Randrianirina, ya ce a shirye yake ya tattauna da ƙungiyar Tarayyar Afirka, wadda ta dakatar da ƙasar daga cikinta saboda kifar da gwamnatin Andry Rajoelina.

"Ba mu yi mamakin matakin da aka ɗauka ba. (Amma) daga yanzu, za mu yi tattaunawar sulhu ta bayan-fage. Za mu ga yadda za ta kaya," in ji Kanar Michael Randrianirina a wani taron manema labarai da ya jagoranta ranar Alhamis.

Randrianirina ya ce zai sha rantsuwar kama aiki ranar Jumma’a a gaban Babbar Kotun Tsarin Mulki ta ƙasar a Antananarivo, babban birnin ƙasar.

Sai dai a ranar Alhamis, Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres ya yi Allah wadai da juyin mulkin da sojoji suka yi wa gwamnatin farar-hula a ƙasar, inda ya yi kira a dawo da tsarin mulki da doka.

"Ina yin tir da kawar da gwamnati da ƙarfin soji a Madagascar kuma ina kira a dawo da tsarin mulki da doka," a cewar Guterres a wata sanarwa da ya wallafa.

"Ina bayar da shawara ga dukkan masu rua da tsaki na Malagascar, ciki har da matasa su yi aiki tare domin magance matsalolin da suka haddasa yamutsi a ƙasar," in ji shi.

Ya ƙara da cewa a shriye MDD take ta yi aiki tare da ‘yan ƙasar da kuma neman goyon bayan ƙasashen duniya domin maido da tsarin mulki da oda.

Rajoelina, wanda ‘yan majalisar dokokin ƙasar suka tsige bayan ya tsere daga ƙasar, inda ya nuna fargaba game da yiwuwar halaka shi sakamakon zanga-zangar da matasa suka kwashe makonni suna yi wadda sojoji suka goyi bayanta, ya soki matakin Randrianirina na ɗarewa karagar mulki ƙasar.

Rumbun Labarai
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar