| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Majalisar Shura ta Kano ta zauna da Malam Lawan Triumph don jin bahasi
Kwamitin Majalisar Shura na Jihar Kano ya ci gaba da aiki kan ƙorafe-ƙorafen da aka gabatar wa majalisar game da wa'azin sanannen malamin addinin Musuluncin, Sheikh Lawan Abubakar Shu'aibu, da aka fi sani da Lawan Triumph.
Majalisar Shura ta Kano ta zauna da Malam Lawan Triumph don jin bahasi
An saurari bahasin malin ranar Litinin 13 ga Oktoba a Kano
13 Oktoba 2025

A Jihar Kano da ke arewacin Nijeriya, Majalisar Shura ta jihar ta yi wani zama na musamman da sanannen malamin addinin Musulunci da ke jihar, Sheikh Abubakar Shu’aibu Lawan

Malamin da aka fi sani da Lawan Triumph ya bayyana a gaban majalisar a wani zama da ya gudana a ofishin hedikwatar hukumar tsaro ta farin kaya, DSS reshen jihar Kano.

Zaman ya gudana ne ƙarƙashin Shugaban Majalisar Shurar, Wazirin Kano Malam Sa’ad Shehu Giɗaɗo, tare da taimakon sakataren majalisar da sauran ‘yan kwamitin binciken da aka kafa a baya.

Sauran mahalarta zaman sun haɗa da wakilan hukumomin tsaro a jihar, da manema labarai.

Tun makonni da suka wuce ne ƙungiyoyin addini a jihar suka gabatar da ƙorafe-ƙorafe a gaban majalisar kan wasu kalamai da mai wa'azin ya yi dangane da Annabi Muhammad (SAW).

Yadda zama ya kasance

Rahotanni sun ce, yayin zaman an kunna wa malamin wa’azozin da aka yi ƙorafi kansu har guda huɗu, inda ya tabbatar da cewa muryarsa ce, sannan aka gabatar masa da tambayoyi game da kalamansa cikin karatuttukan.

A jawabinsa, Sheikh Triumph ya ce, “Ƙofarmu a buɗe take musamman ni. Almajirinku ne ɗanku ne, a duk lokacin da aka ga abin da ba daidai ba wanda na yi, za a iya kira na.

“Wallahi ga duk waɗanda suka san ni, zan iya takowa in zo gidan kowane ne a cikin malamai a matsayin gidana ne, gidanmu ne, don in zo in ji nasiha kuma in ji faɗakarwa”, in ji malamin.

Daga bisani malamai daban-daban sun gabatar masa da nasiha da shawarwari, yayin da Sheikh Lawan Triumph ya gode wa kwamitin da gwamnatin Kano.

A ƙarshen zaman, kwamitin ya bayyana cewa zai miƙa rahoton zaman ga gwamnatin Kano domin ɗaukar mataki na gaba.

Rumbun Labarai
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso