| hausa
AFIRKA
1 minti karatu
Hatsarin kwale-kwale ya kashe mutane 15 a Ghana
Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa kwale-kwalen ya yi lodi ne fiye da ƙima, a cewar hukumomi.
Hatsarin kwale-kwale ya kashe mutane 15 a Ghana
Mutane 15 sun mutu sakamakon kifewar kwale-kwale a Ghana kuma galibinsu kananan yara ne: hukumomi
13 Oktoba 2025

Wani kwale-kwale dauke da fasinjoji ya kife a tafkin da ke arewa maso gabashin Ghana, inda ya kashe mutum 15 waɗanda akasarinsu ƙananan yara ne, kamar yadda hukumomin da ke kula da harkokin ruwa suka sanar.

“Abin takaici, mutum 11 daga cikin wadanda suka mutu yara ne ‘yan tsakanin shekaru biyu zuwa shekaru 14 (maza biyar da mata shida)” a hatsarin da ya afku a ranar Asabar a Tafkin Volta da ke gundumar Krachi ta Yamma a yankin Oti, a cewar wata sanarwa da Hukumar da ke kula da ruwa ta Ghana ta fitar a ranar Lahadi.

Yaran da sauran wadanda abin ya rutsa da su wadanda suka kusan kai shekaru 64, suna kan hanyar Okuma zuwa Bovime ne a lokacin da kwale-kwalen ya kife, in ji sanarwar.

Mutum hudu daga cikin manyan sun tsira da ransu, a cewar sanarwar, tana mai bayyana hatsarin a matsayin mai “mai muni kana wanda ya keta ka’idojin tsaro da aka gindaya’’.

Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa kwale-kwalen ya yi lodi ne fiye da ƙima, a cewar hukumar.

An tura wata tawagar bincike ta musamman, ciki har da sojojin ruwa domin tantance musabbabin lamarin.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher