AFIRKA
2 minti karatu
Ƙungiyar AU ta dakatar da Madagascar daga cikinta sakamakon juyin mulki a ƙasar
Shugaban Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) Mahamoud Ali Youssouf ya ce dakatarwar za ta soma aiki ne nan-take.
Ƙungiyar AU ta dakatar da Madagascar daga cikinta sakamakon juyin mulki a ƙasar
Shugaban AU Mahamoud Ali Youssouf
16 Oktoba 2025

Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta dakatar da Madagascar daga cikinta sa'o'i kaɗan bayan da jagoran juyin mulkin soji a ƙasar ya ce za a rantsar da shi a matsayin shugaban ƙasar.

“Dole a bi tsarin doka maimakon amfani da ƙarfin soji,” a cewar shugaban ƙungiyar AU Mahamoud Ali Youssouf a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, yana mai ƙari da cewa dakatarwar za ta soma aiki ne nan-take.

Shugaba Andry Rajoelina ya tsere daga ƙasar, saboda fargabar tsaron rayuwarsa bayan shafe makwanni ana zanga-zangar ƙin jinin gwamnati mai taken ‘‘Gen-Z’’, wadda ɓangaren soji suka goyi baya kan ƙarancin ruwa da wutar lantarki, kana matakin korar ɗaukacin majalisar gwamnatinsa da ya yi, ya ƙara dagula lamarin wanda ya kai ga kira da ya yi murabus.

Masu AlakaTRT Afrika - Shugaban Madagascar na ɓuya a wani 'wuri mai aminci' bayan mummunar zanga-zangar da ta ɓarke a ƙasar

Daga wani wuri da ba a bayyana ko ina ne ba, ya yi yunƙurin rusa majalisar dokoƙin ƙasar ta hanyar doka.

Majalisar ta yi watsi da dokar inda ta kaɗa ƙuri’ar tsige shi a ranar Talata.

Jim kaɗan bayan haka ne, Kanar Michael Randrianirina da jiga-jigan rundunarsa ta CAPSAT suka ba da sanarwar cewa sojoji sun karɓe iko, kana aka sanar da rusa yawancin cibiyoyin gwamnati kuma kafa gwamnatin riƙon kwarya.

Kada a ƙara asarar rayuka

Randrianirina ya shaida wa manema labarai a ranar Laraba cewa nan ba da jimawa ba za a rantsar da shi a matsayin shugaban ƙasa bayan da babbar kotun tsarin mulkin ƙasar ta gayyace shi da ya yi wannan aiki.

Kazalika, a ranar Larabar ne, ƙungiyar raya ƙasashen kudancin Afirka ta SADC, ta zaɓi wani kwamitin dattawa a wani yunƙuri na kawar da tashe-tashen hankula a ƙasar da Faransa ta yi wa mulkin mallaka.

Wata sanarwa da shugaban ƙasar Malawi Peter Mutharika, wanda shi ne shugaban ƙungiyar sashen SADC da ke kula da harkokin siyasa da tsaro da kuma haɗin gwiwar tsaro ya fitar ta ce, tsohuwar shugabar ƙasar Malawi Joyce Banda ce za ta jagoranci kwamitin da zai mayar da hankali wajen cim ma zaman lafiya da tattaunawa a ƙasar da ke yankin tsibirin.

"Ba za a ƙara asarar rayuka wani ɗan kasa ba saboda tashin hankalin," in ji Mutharika.

Rumbun Labarai
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan