| hausa
SIYASA
2 minti karatu
Burkina Faso ta kama ma’aikatan jinƙai bisa zargin leƙen asiri
An zargi jami’an leƙen asirin da daukar bayanai masu muhimmanci a na’urori game da rundunar sojin kasar ta Yammacin Afirka.
Burkina Faso ta kama ma’aikatan jinƙai bisa zargin leƙen asiri
Kyaftin Ibrahim Traore ya shiga ofis a matsayin shugaban kasar Burkina Faso a watan Satumban 2022. /AA
8 Oktoba 2025

Gwamnatin Burkina Faso ta ce ta kama ma’aikatan jinƙai takwas bisa tuhumar leƙen asiri, inda ta zarge su da ɗaukan bayanai masu muhimmanci na ƙasar tare da bai wa ƙasashen waje.

Ma’aikatan su takwas na aiki da Ƙungiyar Ƙasa da Ƙasa Mai Zaman Kanta ta INSO, ƙungiyar da ke da cibiya a Holland kuma take bayar da taimakon jinƙai.

Ƙungiyar ta tattara tare da naɗar muhimman bayanai game da sojojin ƙasar ta Yammacin Afirka, ciki har da yankunan da ake kai farmakai, hanyoyin jerin gwanon motoci da yawan jami’an da ake kai wa, in ji Ministan Tsaro Mahamadou Sana, a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata..

Daga cikin wadanda aka kama har da ‘yan ƙasar Faransa biyu, ciki har da daraktan INSO a Burkina Faso, da wani ɗan kasar Czech, da ɗan ƙasar Mali da ‘yan Burkina Faso huɗu, in ji Ministan.

Bai bayyana takamaiman yaushe ne aka yi kamen ba.

INSO ta bayyana a ranar Talata cewa suna tattara bayanai ne kawai don sanya ido kan tsaro da kare ma’aikatan agaji.

“Bayanan da muka tattara ba na sirri ba ne kuma waɗanda jama’a suka riga suka sani ne,” in ji kungiyar.

INSO ta kuma aƙra da cewa tana bayar da cikakken haɗin kai ga mahukuntan Burkina Faso a binciken da suke yi, kuma tana aiki don ganin an saki ma’aikatan nata da aka tsare.

Burkina Faso na yaƙi da ta’addanci da ya taɓarɓara al’amura a ƙasar ta Yammacin Afirka tsawon shekaru.

 

Rumbun Labarai
Shugabar ƙasar Tanzania Samia Hassan ta sha rantsuwar kama aiki a wa’adi na biyu
Kutungwilar Netanyahu kan tsagaita wuta a Gaza ita ce ci gaba da kashe Falasdinawa
Zaben Tanzania: Intanet ya katse sannan zanga-zanga ta barke a ranar zabe
Masu nazarin kayan tarihi sun gano kisan gillar Faransa a wata makabartar Senegal
Mahama ya hana ministoci bayyana manufofin gwamnatin Ghana sai da izinin majalisar ministoci
Shugaban Sudan al Burhan ya ce ‘sojojin ƙasar sun janye’ daga Al Fasher
Hamas na aiki da yarjejeniyar tsagaita wuta amma Isra'ila na ci gaba da karya ta, in ji Erdogan
Ghana tana alhinin mutuwar matar tsohon shugaban ƙasar, Nana Konadu Agyeman-Rawlings
Kotu a Bangladesh ta tura manyan hafsoshin soji gidan yari a wata shari’a ta tarihi
Tsohon shugaban Faransa Nicolas Sarkozy ya fara zaman  gidan kaso kan karɓar kuɗin a wurin Gaddafi
Firaministan Falasɗinu ya bayyana shirin ware dala biliyan 65 don sake gina Gaza
Tsohon Firaministan Kenya Raila Odinga ya mutu a India
Shugaban Madagascar na ɓuya a wani 'wuri mai aminci' bayan mummunar zanga-zangar da ta ɓarke a ƙasar
Yadda diflomasiyyar Erdogan na Turkiyya ta taimaka wajen cim ma tsagaita wuta a Gaza
Shekaru biyu na kisan kiyashin Isra’ila a Gaza: Yadda Amurka ke kare Netanyahu daga tuhuma
Swahili ne mafita ga Gabashin Afirka ba Faransanci ba
Za a ƙaddamar da shirin bayar da lasisin bindiga na intanet a Ghana
ICC: Yaudara daga wadanda suka kafa ta, mafaka ga mambobin ƙasashen Afirka
Fayyaceccen bayanin Erdogan a MDD: Gaza, 'ƙasar Isra'ila', da makomar yankin
Mene ne daftarin Babban Zauren MDD kan mafitar samar da ƙasashe biyu da ƙarara ya yi watsi da Hamas?