| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Wani harin da ake zargin na RSF ne ya kashe aƙalla mutum shida a sansanin ‘yan gudun hijirar Sudan
Kicin ɗin, waɗanda ake kira Takaya, wuri ne da ke cike da jama’a inda ake raba abinci ga mutanen da aka kora daga gidajensu a Al Fasher da ma wasu wuraren da ake rikici.
Wani harin da ake zargin na RSF ne ya kashe aƙalla mutum shida a sansanin ‘yan gudun hijirar Sudan
Al Fasher ya fuskanci arangama mai tsanani tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF tun watan Mayun shekarar 2024.RSF / AP
1 Oktoba 2025

Aƙalla fararen-hula shida ne aka kashe yayin da aka jikkata 24 a wani harin na manyan bindigogi da aka kai wani sansanin ‘yan gudun hijira a Al Fasher da ke Yammacin Sudan, kamar yadda wani kwamitin jinƙai na ƙasar ya bayyana, inda ya zargi dakarun RSF da kai harin.

“A yau, RSF ta kai hari kan jerin kicin na abinci a Al Fasher, inda ta kashe fararen-hula shida kuma ta jikkata sama da wasu 24,” in ji kwamitin da ke jagorantar gwagwarmaya a Al Fasher a wata sanarwar da ta fitar ranar Talata.

“Har kicin ɗin da ke kasancewa mafaka ga talakawa da masu jin yunwa ma bai tsira daga harin RSF ba. An lalata tukwane kuma aka baza abinci a ƙasa, tamkar ƙaddamar da yaƙi kan masu rauni da masu jin yunwa ne,” a cewar sanarwar.

Jerin kicin  ɗin – wanda ake kira Takaya – wuri ne na al’umma wanda ke ba da abinci ga mazauna wurin da waɗanda aka raba da muhallansu a Al Fasher da ma wasu wuraren da ake yaƙi wanda ‘yan sa-kai ne ke tafiyar da shi da tallafin masu taimaka wa jama’a da ƙungiyoyin ba da agaji.

Gwamnan yankin Darfur Minni Arko Minnawi ya ce kai hari kan ɗaya daga cikin sansanonin ‘yan gudun hijira a Al Fasher da mayaƙan rundunar RSF suka yi ya nuna “wani sabon laifi da ya ƙaru kan tarihinta na zubda jinin fararen hula mara makamai.”

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher