AFIRKA
2 minti karatu
Wani harin da ake zargin na RSF ne ya kashe aƙalla mutum shida a sansanin ‘yan gudun hijirar Sudan
Kicin ɗin, waɗanda ake kira Takaya, wuri ne da ke cike da jama’a inda ake raba abinci ga mutanen da aka kora daga gidajensu a Al Fasher da ma wasu wuraren da ake rikici.
Wani harin da ake zargin na RSF ne ya kashe aƙalla mutum shida a sansanin ‘yan gudun hijirar Sudan
Al Fasher ya fuskanci arangama mai tsanani tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF tun watan Mayun shekarar 2024.RSF / AP
1 Oktoba 2025

Aƙalla fararen-hula shida ne aka kashe yayin da aka jikkata 24 a wani harin na manyan bindigogi da aka kai wani sansanin ‘yan gudun hijira a Al Fasher da ke Yammacin Sudan, kamar yadda wani kwamitin jinƙai na ƙasar ya bayyana, inda ya zargi dakarun RSF da kai harin.

“A yau, RSF ta kai hari kan jerin kicin na abinci a Al Fasher, inda ta kashe fararen-hula shida kuma ta jikkata sama da wasu 24,” in ji kwamitin da ke jagorantar gwagwarmaya a Al Fasher a wata sanarwar da ta fitar ranar Talata.

“Har kicin ɗin da ke kasancewa mafaka ga talakawa da masu jin yunwa ma bai tsira daga harin RSF ba. An lalata tukwane kuma aka baza abinci a ƙasa, tamkar ƙaddamar da yaƙi kan masu rauni da masu jin yunwa ne,” a cewar sanarwar.

Jerin kicin  ɗin – wanda ake kira Takaya – wuri ne na al’umma wanda ke ba da abinci ga mazauna wurin da waɗanda aka raba da muhallansu a Al Fasher da ma wasu wuraren da ake yaƙi wanda ‘yan sa-kai ne ke tafiyar da shi da tallafin masu taimaka wa jama’a da ƙungiyoyin ba da agaji.

Gwamnan yankin Darfur Minni Arko Minnawi ya ce kai hari kan ɗaya daga cikin sansanonin ‘yan gudun hijira a Al Fasher da mayaƙan rundunar RSF suka yi ya nuna “wani sabon laifi da ya ƙaru kan tarihinta na zubda jinin fararen hula mara makamai.”