| hausa
AFIRKA
3 minti karatu
Zanga-zangar neman ingantaccen ilimi da kiwon lafiya ta matasan Maroko ta shiga kwana na huɗu
Haɗakar gwamnati ta bayyana amincewarta da tattaunawa da matasan cikin hukumomi da wurare na gwamnati domin samun mafita na gaske.
Zanga-zangar neman ingantaccen ilimi da kiwon lafiya ta matasan Maroko ta shiga kwana na huɗu
“Mutane suna son a kawo ƙarshen cin hanci da rashawa,” kamar yadda masu zangazanga suka yi ta rerawa a waƙa. / Photo: Reuters
1 Oktoba 2025

Zanga-zangar da matasa ke jagoranta mai neman a inganta ilimi da kiwon lafiya a ƙasar Maroko ta kai ga arangama da jami’an tsaro, inda aka shiga kwana na huɗu a jere na zanga-zanga a faɗin ƙasar.

Ana tsara zanga-zangar ne ta intanet inda ake amfani da kafafen TikTok da  Instagram da kuma manhajar gem ta intanet ta Discord.

A biranen kudancin ƙasar na Tiznit da Inzegane da Ait Amira da kuma biranen gabashin ƙasar na Oujda da Temara kusa da babban birnin ƙasa Rabat, ɗaruruwan matasa masu zanga-zanga sun yi ta jifan dakarun tsaro da ke neman tarwatsa su, kamar yadda kafafen watsa labaran ƙasar da shaidun gani da ido suka bayyana.

A Ait Amira, da ke da nisan kilomita 560 kudu da Rabat, masu zanga-zanga sun kayar tare da ƙona motocin jami’an tsaro da kuma ƙona wani banki, kamar yadda bidiyon da aka wallafa shafukan sada zumunta ya nuna.

A Inzegane, bidiyon da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna masu zanga-zanga sanye da takunkumin rufe fuska sun ƙona banki yayin da wasu ke arangama da ‘yan sanda da ke watsa ruwan zafi.

An ƙona wasu motoci, da kuma wani gungun masu zanga-zanga da suka yi ƙoƙarin kutsa cikin wani babban kanti, in ji shaidu da kuma bidiyon da aka wallafa a shafukan sada zumunta.

‘Ƙarshen cin hanci da rashawa’

A can Tiznit da ke kudancin kuma gomman masu zanga-zanga sun wurga duwatsu kan jami’an tsaro yayin da suke ƙoƙarin tarwatsa jerin gwanon, kamar yadda shaid suka shaida wa kamfanin dillancin labaran Reuters.

Masu zanga-zanga sun rera take iri-iri ciki har da “Mutane na son a kawo ƙarshen cin hnaci da rashawa,” in ji su.

A Oujda, wani mai zanga-zanga ya ji rauni mai muni bayan wata motar jami’an tsaro ta kaɗe shi, kamar yadda kamfanin dillancin labaran ƙasar MAP ya ruwaito.

A birnin Rabat, ‘yan sanda sun kama gomman matasa yayin da suka fara rera take a wata unguwa mai tarin jama’a, kamar yadda wani shaidan Reuters ya bayyana.

Ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Maroko (AMDH) an ba da belin matasa 37, zuwa lokacin da za a kammala bincike.

Hakim Saikuk, shugaban ɓangaren AMDH a Rabat, ya yi Allah wadai da kamen a matsayin wani abu da ya saɓa wa tsarin mulki.

A Casablanca, msu zanga-zanga 24 da suka tare babban titi ranar Lahadi sun kasance a ƙarƙashin bincike na shari’a, kamar yadda mai gabatar da ƙara na gwamnati ya bayyana.

Haɗaka ta gwamnati ta fitar da wata sanarwa ranar Talata inda ta bayyana yardarta da shiga tattaunawa da matasan "cikin hukumomi da kuma wurare na gwamnati domin a a samar da mafita na gaskiya".

Ta kuma yaba wa abin da ta kira "martanin mai daidaito na jami’an tsaro bisa tsare-tsaren doka."

Ma’aikatar tsaron cikin gida ba ta yi tsokaci kan lamarin nan take ba.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher