| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Sojojin Sudan sun sake ƙwace muhimman wurare daga dakarun RSF a El-Fasher
Wata sanarwa da rundunar sojin Sudan ta fitar ta ce dakarunta sun kai farmaki a wurare daban-daban da ke hannun mayaƙan RSF a El-Fasher inda suka sanya su yin asarar dakaru da kayayyakin aiki.
Sojojin Sudan sun sake ƙwace muhimman wurare daga dakarun RSF a El-Fasher
Dakarun sojin Sudan suna ci gaba da ƙwace muhimman yankuna daga hannun mayaƙan RSF
8 Oktoba 2025

Rundunar sojin Sudan ta ce ta ƙwato yankuna da dama da ke ƙarƙashin mayaƙan rundunar ko-ta-kwata ta Rapid Support Forces (RSF) a El-Fasher, babban birnin Jihar North Darfur da ke yammacin Sudan.

Wata sanarwa da rundunar sojin Sudan ta fitar ta ce dakarunta sun kai farmaki a “wurare daban-daban” da ke hannun mayaƙan RSF a El-Fasher inda suka sanya su yin asarar dakaru da kayayyakin aiki.

Kazalika rundunar sojin ta ce dakarun nata sun ƙwace motocin yaƙi da dama, ko da yake ba ta faɗi adadinsu ba, amma ta ƙara da cewa sun lalata motocin yaƙi shida, ciki har da motoci masu sulke.

A cewar rundunar sojin, mayaƙan RSF sun ƙaddamar da hari a kudacin El-Fasher, amma sojojin gwamnati sun daƙile harin sannan suka haddasa musu asara mai yawa.

Kawo yanzu rundunar RSF ba ta yi raddi game da sanarwar sojojin Sudan ba.

An yi wa El-Fasher ƙawanya

Dakarun RSF sun yi wa yankin El-Fasher ƙawanya tun ranar 10 ga watan Mayun 2024, duk da gargaɗi da ƙasashen duniya suka yi game da hatsarin yi wa birnin ƙawanya, wanda ya kasance cibiyar ayyukan agaji ga jihohi biyar da ke Darfur.

El-Fasher yanki ne da ke da matuƙar muhimmanci, don haka ƙwacewar da dakarun soji suka yi masa za ta kasance wani babban koma-baya ga dakarun RSF. Dakarun na RSF sun rasa wurare da dama tun bayan da rundunar sojin Sudan ta fatattake su daga Khartoum a watan Agusta.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher