| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
An yanke wa wani mutum hukuncin kisa kan zagin shugaban ƙasar Tunisia a Facebook
Lauyan wanda aka yanke wa hukuncin ya ce mutumin ba shi da wani cikakken ilimi sannan abubuwan da ya rinƙa wallafawa a Facebook akasari kwafo su ya rinƙa yi daga wasu shafuka domin jawo hankalin gwamnati kan mawuyacin halin da jama'ar ƙasa ke ciki.
An yanke wa wani mutum hukuncin kisa kan zagin shugaban ƙasar Tunisia a Facebook
Shugaban Tunisiya Kais Saied
4 Oktoba 2025

Wata kotu a Tunisiya ta yanke hukuncin kisa kan wani mutum mai shekaru 51 saboda irin abubuwan da ya rinƙa wallafa a Facebook waɗanda ake gani a matsayin cin mutuncin Shugaba Kais Saied kuma suna barazana ga tsaron ƙasa, in ji lauyansa a ranar Juma’a.

An yanke wa wanda ake zargin, wanda ba a bayyana sunansa ba, hukunci ranar Laraba bisa tuhume-tuhume uku: yunkurin kifar da gwamnati, zagin shugaban ƙasa, da kuma yaɗa bayanan ƙarya ta yanar gizo.

Alkalai sun ce wallafe-wallafen sun tayar da tarzoma da rikici, kuma sun saɓa wa dokar laifuka ta Tunisiya da kuma dokar laifukan yanar gizo ta 2022, wato Decree 54. Wannan hukuncin shi ne irinsa na farko a Tunisiya.

Duk da cewa akwai hukuncin kisa a cikin dokokin laifuka na Tunisiya, kuma kotunan farar hula suna yanke irin wannan hukunci lokaci zuwa lokaci, rabon da a aiwatar da wannan hukunci tun a 1991 a lokacin da aka kashe wani mutum wanda ya shahara wurin kashe mutane.

Ƙarancin tasiri a yanar gizo

A wata sanarwa da ya wallafa a Facebook, lauyansa Oussama Bouthelja ya ce wanda yake karewa yana tsare tun watan Janairun 2024 kafin a fara shari’a.

Ya ce mahaifin yara uku ne, kuma yana aiki ne kawai a matsayin ɗan ƙwadago lokaci-lokaci, yana fama da nakasa ta dindindin da ya samu sakamakon hatsarin da ya faru da shi a wurin aikin.

Bouthelja ya bayyana shi a matsayin wanda ba shi da ilimi sosai kuma ba shi da tasiri sosai a yanar gizo.

“Yawancin abubuwan da ya wallafa ya kwafe su ne daga wasu shafuka, kuma wasu daga cikin wallafe-wallafen ba su samu wani martani ba kwata-kwata,” in ji Bouthelja.

“A kotu, ya ce niyyarsa ita ce jawo hankalin hukumomi kan mawuyacin halin rayuwarsa, ba wai tayar da tarzoma ba.”

Wannan hukuncin shi ne na baya-bayan nan da aka yi amfani da Decree 54, wata doka da ta haramta “ƙirƙira, yadawa, watsawa ko rubuta labaran ƙarya ... da nufin keta haƙƙin wasu, cutar da tsaron jama’a ko tsaron ƙasa, ko kuma cusa fargaba a tsakanin al’umma.”

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher