| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
RSF ta kai hari da jirgi maras matuƙi na ƙunar baƙin-wake kan fararen-hula a Sudan – Sojoji
Rundunar Sojin Sudan ta zargi ƙungiyar RSF da kai hari kan fararen-hula a Kordofan ta Arewa da ke kudancin Sudan ta hanyar amfani da jirgi maras matuƙi.
RSF ta kai hari da jirgi maras matuƙi na ƙunar baƙin-wake kan fararen-hula a Sudan – Sojoji
Ba a samu rahoton asarar rayuka daga harin ba
5 Oktoba 2025

Rundunar Sojin Sudan ta zargi dakarun Rapid Support Forces (RSF) a ranar Lahadi da kai hare-haren jirgi maras matuƙi kan wuraren fararen-hula a jihar Kordofan ta Arewa da ke kudancin Sudan.

A cikin wata sanarwa da sojojin suka fitar, sun bayyana cewa dakarun RSF sun kai hari kan wasu wuraren fararen hula a birnin El-Obeid, babban birnin jihar, ta hanyar amfani da jiragi maras matuƙi na ƙunar baƙin-wake, inda suka lalata Asibitin Al-Dhaman, wasu unguwannin jama’a da wasu gine-gine a ranar Asabar da dare.

Ba a samu rahoton asarar rayuka daga harin ba

Sojojin Sudan sun bayyana harin da RSF ta kai a matsayin wata alama da ke nuna yadda kungiyar ta ‘yan tawaye ke ci gaba da karya dokokin jin kai na ƙasa da ƙasa tare da cutar da fararen hula marasa laifi.

Sojojin sun ƙara ƙwace iko

Babu wani martani kai tsaye daga RSF kan wannan sanarwa ta sojojin.

Hari na baya-bayan nan ya zo ne a daidai lokacin da yankunan da RSF ke riƙe da su ke kara raguwa cikin sauri a makonnin da suka gabata, yayin da sojojin ke ƙara ƙarfin iko a jihohin Khartoum, White Nile, da Kordofan ta Arewa.

A halin yanzu, kasancewar RSF ta taƙaita ne kawai a wasu yankuna na Kordofan ta Yamma, Kordofan ta Kudu, da jihohin Blue Nile, tare da wasu sassan jihohi hudu daga cikin biyar na Darfur.

Tun daga tsakiyar watan Afrilu na shekarar 2023, sojojin Sudan da RSF ke fafatawa a wani yaƙi da har yanzu an kasa yin sulhu duk da mawuyacin halin jin kai da ƙasar ke ciki.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher