| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
'Yan bindiga sun kashe aƙalla mutum 14 a sansanin ‘yan gudun hijira na DR Kongo
Harin da aka kai a yankin Djugu ya afku ne a ranar Alhamis a daidai lokacin da mutanen da suka rasa matsugunansu daga yankin Rhoo ke kan hanyarsu ta zuwa gonakinsu a ƙauyukan da ke kewaye, a cewar rahoton.
'Yan bindiga sun kashe aƙalla mutum 14 a sansanin ‘yan gudun hijira na DR Kongo
Har yanzu babu wata sanarwa a hukumance kan lamarin.
3 Oktoba 2025

Aƙalla mutane 14 ne aka kashe a wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a sansanin ‘yan gudun hijira a lardin Ituri na Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo, kamar yadda kafafen yada labarai na ƙasar suka bayyana.

Harin da aka kai a yankin Djugu ya afku ne a ranar Alhamis a daidai lokacin da mutanen da suka rasa matsugunansu daga yankin Rhoo ke kan hanyarsu ta zuwa gonakinsu a ƙauyukan da ke kewaye, a cewar rahoton.

Gidan rediyon Majalisar Ɗinkin Duniya, ya shaida wa manema labarai cewa, waɗanda harin ya rutsa da su manoma ne, ya kuma danganta harin da ƙungiyar ‘yan tawayen Cooperative for Development of Congo (CODECO).

“Shaidu sun ruwaito cewa ‘yan tawayen sun yi wa manoman kwanton ɓauna ne, kana suka buɗe wuta tare da jikkata wasu ta hanyar yankar su da wuƙaƙe, akwai yiwuwar adadin ya zarce haka saboda ba tsoron iya shiga yankin,” in ji rahoton.

Fargaba a sansanin

Har yanzu babu wata sanarwa a hukumance kan lamarin.

Bayan harin, fargaba ta mamaye yankin na Rhoo, wanda ke ɗauke da dubban mutanen da suka rasa matsugunansu, a cewar rahoton.

Shugabannin ƙungiyoyin fararen-hula na yankin sun yi kira ga sojoji su gaggauta shiga tsakani domin tabbatar da tsaron yankin.

Ƙasar Kongo dai ta fuskanci ɗaya daga cikin rikice-rikice mafi daɗewa da aka ganin inda mutane miliyan 7 suka rasa matsugunansu a ƙasar, a cewar MDD.

Ƙungiyoyin da ke ɗauke da makamai suna yawan kai hari kan fararen hula a gabashin Kongo.

A watan Yuli kadai Majalisar Dinkin Duniya ta tattara munanan hare-haren ƙungiyar Allied Democratic Forces (ADF), da na CODECO da kuma na mayakan sa kai na Raia Mutomboki/Wazalendo a Ituri, da Kivu ta Kudu da kuma Arewacin Kivu.

 

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher