| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
“An umarci jami’an tsaronmu da jami’an leƙen asiri su gano, tare da kuɓutar da ɗaliban da kuma dawo da su cikin aminci,” a cewar Minitstan Watsa Labarai na Kasar, Mohammed Idris a cikin wata sanarwa.
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami'an tsaro su gaggauta ganowa da kuma kubutar da daliban da aka sace
18 Nuwamba 2025

Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaron kasar su kubutar da ‘yan matan da wasu ‘yan bindiga suka sace a jihar Kebbi a farkon makon nan.

Ministan Watsa Labarai na kasar Mohammed Idris ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shainsa na X ranar Litinin.

“An umarci jami’an tsaronmu da jami’an leken asiri su gano, tare da kubutar da daliban da kuma dawo da su cikin aminci,” a cewar minitstan.

Ya kara da cewa, “Gwamnatin Tarayya ba za ta saurara ba har sai an cim ma wannan buri.”

A cikin daren Litinin din da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga suke kai hari a Makarantar Sakandare ta ’Yan Mata ta Gwamnati da ke Maga a Ƙaramar Hukumar Danko/Wasagu, inda suka kashe mataimakin shugaban makarantar, suka kuma tafi da dalibai mata 25, a cewar runduna ‘yan sandan jihar Kebbi.

Rundunar ta ce bayan faruwar lamarin, Kwamishinan ‘Yan Sanda, Bello Muhammad Sani, ya tura jami’an ‘yan sanda na musamman tare da jami’an soji da ƙungiyoyin ‘yan bijilanti zuwa yankin.

A sanar da ministan watsa labaran ya fitar, ya ce, gwamnatin tarayya ta damu sosai da faruwar lamarin, sannan tana tare da iyalan wadanda abin ya shafa.

 Mohammed Idris ya ce gwamnati na sauya fasallin sojojin kasar, da ‘yan sanda da hukumomin leken asiri, ta yadda za su iya hana sake aukuwar irin wadannan hare-hare, tare da mayar da martani cikin gaggawa a duk lokacin da aka samu matsala irin wannan.

Ya kara da cewa Nijeriya tana jaddada hadakarta da kawayenta a yankin, ta hanyar ECOWAS, da Kungiyar Tarayyar Afirka da Dakarun Hadin Gwiwa na Kasa da Kasa, “don tsare kan iyakokinmu da kuma hana kungiyoyin masu aikita laifuka walwala.”

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?