| hausa
NIJERIYA
1 minti karatu
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Bayanai na cewa, maharan sun afka makarantar ne da misalin karfe biyu zuwa uku na dare, inda suka tafi da dalibai da ma’aikatan, sai dai har kawo yanzu babu bayani kan adadin mutanen da harin ya shafa.
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Gwamnan Jihar Niger Mohammed Umar Bago
21 Nuwamba 2025

Rahotanni daga Jihar Neja a arewa ta tsakiyar Nijeriya na cewa, yan bindiga sun sace daliba da ma’aikatan wata a Makarantar St. Mary a karamar hukumar Agwara a Jihar Neja cikin daren Juma’a.

Kawo yanzu babu cikakken bayani kan adaddin mutanen da aka sace, sai dai gwamnatin jihar ta Neja ta tabbatar da lamarin a wata sanarwa da ta fitar, sai dai ba ta yi karin bayani ba.

Ita ma rundunar ‘yan sandan jihar ta Neja ba ta kai ga fitar da bayani kan lamari ba, sai dai kakakin runduna ya shaida wa manema labarai a kasar cewa zai bayar da cikakken bayani nan gaba.

Bayanai na cewa, maharan sun afka makarantar ne da misalin karfe biyu zuwa uku na dare, inda suka tafi da dalibai da ma’aikatan.

Sace daliban a makaranta a jihar neja dai na zuwa ne kasa da mako guda da sace wasu dalibai mata 25 a makarantar sakandaren gwamnati a Jihar Kebbi, da kai hare-hare a jihar Kwara, abin da ya tilasta rufe makarantu fiye da 50 a Jihar ta Kwara.

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?