| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Tun bayan zargin da Amurka ta yi kan kashe Kiristoci a Nijeriya, gwamnatin ƙasar ta musanta wannan zargin amma duk da haka Amurka ta ci gaba da tafiya a kan ra’ayinta kan cewa ana zaluntar Kiristoci a Nijeriya.
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Babban Mai Bai wa Shugaban Nijeriya Shawara kan Tsaro Nuhu Ribadu
20 Nuwamba 2025

Babban Mai Bai wa Shugaban Nijeriya Shawara kan Tsaro Nuhu Ribadu ya jagoranci wata babbar tawaga zuwa Amurka kan zargin cewa ana zaluntar Kiristoci a Nijeriya.

Zargin ya ƙara karfi ne bayan Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya yi magana kan goyon bayansa ga tsarin samar da ƙasashe biyu masu cin gashin kansu a rikicin Isra’ila da Gaza.

Tun farkon watan nan, Shugaban Amurka Donald Trump ya sake saka Nijeriya cikin jerin ƙasashen da ake sa wa ido na musamman kan walwalar addini, ya kuma bukaci wasu ‘yan majalisa, ciki har da Riley Moore su binciki halin da ake ciki a Nijeriya su dawo masa da sakamako.

Duk da kokarin da Gwamnatin Tarayya ta yi wajen fayyace gaskiya, Amurka ta ci gaba da tafiya a kan ra’ayinta kan cewa ana zaluntar Kiristoci a Nijeriya.

A ranar Talata, an gayyaci mawaƙiyar Amurka Nicki Minaj zuwa Majalisar Dinkin Duniya, MDD don ta yi ƙarin haske kan zargin zaluntar Kiristoci a Nijeriya.

Nijeriya ba ta samu damar halartar taron ba, lamarin da ya sa ta yi korafi.

Sai dai ba a ba Nijeriya damar zuwa wurin taron ba, inda Nijeriyar ta nuna rashin jin daɗinta game da wannan lamarin.

Syndoph Endoni, ƙaramin jakadan dindindin na Nijeriya a MDD, ya ce ware Nijeriya daga tattaunawar — wadda aka gudanar a hedikwatar MDD a New York — tamkar “a aske mana kai ne ba tare da mu ba.”

Taron da Minaj ta halarta an shirya shi ne tare da taimakon Wakiliyar Dindindin ta Amurka a Majalisar Dinkin Duniya.

Amma a ranar Laraba, tawagar Nijeriya ta yi bayanin ainihin halin da ake ciki a ƙasar ga ɗaya daga cikin mutanen da ke yada labarin cewa ana aikata kisan ƙare-dangi a Nijeriya.

Wadanda suka kasance cikin tawagar sun haɗa da Bianca Ojukwu, Ƙaramar Ministar Harkokin Wajen Nijeriya da Kayode Egbetokun, Sufeton ‘Yan Sanda Nijeriya da Lateef Olasunkami Fagbemi, Antoni Janar na Nijeriya da Janar Olufemi Olatunbosun Oluyede, Babban Hafsan Tsaro na Nijeriya da kuma Laftanar Janar EAP Undiendeye, Shugaban Leƙen Asiri na Rundunar Tsaron Nijeriya.

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?