| hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Mai shari’a Emeka Nwite ne ya yanke hukuncin a ranar Laraba bayan samun Ismaila da aka fi sani da Mai Tangaran da laifukan shirya hare-haren ta’addanci a Kano ranar 20 ga Janairun 2021, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 150.
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Jami'an tsaron Nijeriya suna yaƙi da ya 'yan ta'adda a sassan ƙasar
20 Nuwamba 2025

Wata kotun tarayyar Nijeriya a Abuja ta yi wa wani shugaban ƙungiyar ta’addancin ISWAP, Hussaini Ismaila, ɗaurin shekara 20 bisa laifukan ta’addanci.

Mai shari’a Emeka Nwite ne ya yanke hukuncin a ranar Laraba bayan samun Ismaila da aka fi sani da Mai Tangaran da laifukan shirya hare-haren ta’addanci a Kano ranar 20 ga Janairun 2021, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 150.

Da farko, Mai Tangaran ya musa tuhumue-tuhumen da Hukumar Tsaron Farin kaya ta DSS ta gabatar a kansa, amma daga baya ya amsa laifinsa bayan gabatar da shaidu.

Kotun ta yi wa Ismaila ɗaurin shekara 15 a kan tuhuma ta ɗaya, kuma an yi masa ɗaurin shekara 20 a kan tuhuma ta biyu da ta uku da ta huɗu, kuma zai yi zaman kason dukkan ɗaurin ne a lokaci guda, tun daga ranar 31 ga watan Agustan shekarar 2017, lokacin da DSS ta kama shi.

Alƙalin ya kuma ba da umarni ga shugabna Hukumar Gidajen Yari ta Nijeriya da ya tsare mutumin cikin ko wane gidan yarin da ya ga dama, har sai lokacin da ya ƙarasa zaman kasonsa, yana mai ƙarawa da cewa dole a saka a saka shi a shirin gyaran hali da kuma kawar da tsatssauran ra’ayi bayan ya gama zaman kaso kafin ya koma cikin al’umma.

Masu gabatar da ƙara sun ce Ismaila ne ya jagoranci hare-haren da aka kai a shekarar 2012 kan hedikwatar rundunar ‘yan sanda a Bompai, jihar Kano da ofishin shiyya ta daya ta rundunar ‘yan sandan Nijeriya a jihar Kano da ofishin ‘yan sanda da ke unguwar Farm Centre da na Ungwa Uku, duka a jihar Kano, inda aka kashe mutane fiye da 150, wasu daruruwa kuma suka ji rauni.

Jinkirin Shar’ia

Jim kaɗan bayan kama shi a ƙauyen Tsamiyya Babba da ke ƙaramar hukumar Gezawa a jihar Kano a shekarar 2017, an gurfanar da Ismaila a gaban kuliya inda aka tuhume shi da laifuka ƙarƙashin dokar hana ta’addanci ta shekarar 2013.

Shari’arsa ta fuskanci jinkiri daga ɗaukaka ƙara da kuma yin shari’a cikin shari’a, domin tabbatar da gaskiyar cewa wanda ake tuhumar ya yi bayanai ne bisa radin kansa ba bisa tursasawa ba.

A lokacin da aka ci gaba da shari’ar daga baya kuma, masu gabatar da ƙara sun gabatar shaidu biyar, ciki har da jami’an DSS biyu da kuma shaidun gani da ido da suka shaida wasu daga cikin hare-haren.

Ismaila, wanda ya musanta zargin da farko, ya sauya ra’ayi inda ya amsa lafukan bayan kammala gabatar da shaidu.

Daga baya, lauyan wanda ake tuhuman, P. B. daga ƙungiyar lauyoyi masu taimaka wa mutane wato Legal Aid Council (LAC), ya roƙi kotun da ta yi wa mutumin sassauci.

Onijah ya ce Ismaila ya yi nadama kuma ya sauya abin da ya gaya wa kotu domin kada ya ɓata mata lokaci, kuma ya yi nadamar kasancewa da hannu a cikin ta’addanci.

 

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?