| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Janar Shaibu ya bayar da umarnin ne a ranar Litinin, 17 ga Nuwamban 2025, yayin wata ziyarar aiki da ya kai jihar.
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
''Dole ku ceto daliban da aka sace a Kebbi'' in ji Shugaban Sojojin kasa a Nijeriya
18 Nuwamba 2025

Babban Hafsan Sojin Kasa na Nijeriya (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya umarci dakarun soji a karkashin rundunar Operation FANSAN YANMA da su kara himma wajen ceto daliban da aka sace daga Makarantar Sakandare ta 'Yan Mata ta Gwamnati (GGCSS) a karamar Hukumar Danko/Wasagu ta Jihar Kebbi.

Janar Waidi Shuaibu ya bayar da umarnin ne a ranar Litinin, 17 ga Nuwamban 2025, yayin ziyarar aiki da ya kai Jihar ta Kebbi, kwana guda bayan harin da ’yan bindiga suka kai makarantar.

Da yake jawabi ga kwamandoji da sojoji da ke fagen daga, COAS ya bukace su da su kara himma wajen gudanar da ayyukan leken asiri tare da bin diddigin ‘yan bindigar da suka sace daliban.

"Dole ne mu nemo waɗannan yaran. Ku yi aiki cikin hikima da ƙwarewa kan duk wasu bayanan sirri,” in ji Janar Shaibu, yana mai cewa “Babu wani zaɓi a batun yin nasara.”

A wani ɓangare na ziyarar, Janar Shaibu ya kuma gana da 'yan banga da mafarauta na yankin, yana mai bayyana su a matsayin muhimman abokan aiki a wannan lokaci na aikin da ake gudanarwa.

Ya karfafa musu gwiwa da su yi aiki kafada da kafada da sojoji tare da amfani da iliminsu na ƙasa don taimakawa wajen gano masu laifin.

"Tare za mu maido da zaman lafiya da kuma tabbatar da cewa 'ya'yanmu za su iya zuwa makaranta ba tare da tsoro ba," a cewar Babban Hafsan Sojin.

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?