AFIRKA
2 minti karatu
Maroko ta rattaba hannu kan yarjejeniyar yaƙi da cin hanci bayan jerin zanga-zanga a faɗin ƙasar
An sanya hannu kan yarjejeniyoyin ne domin ƙarfafa samar da haɗin kai tsakanin muhimman hukumomi bayan jerin zanga-zangar da matasa suka jagoranta ta neman tsage gaskiya da gyara lamura a ƙasar Maroko.
Maroko ta rattaba hannu kan yarjejeniyar yaƙi da cin hanci bayan jerin zanga-zanga a faɗin ƙasar
Maroko ta rattaɓa hannu kan yarjejeniya ta yaƙi da cin hanci bayan jerin zanga-zangar da aka yi a fadin ƙasar / Reuters
8 Oktoba 2025

Hukumomi a Maroko sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya domin ƙarfafa matakan hanawa da kuma yaƙi da cin hanci da rashawa bayan jerin zanga-zangar da matasa suka jagoranta inda suka nemi a yi gyara kan harkokin gwamnati tare da tsage gaskiya.

Wata sanarwar gwamnati ta ce hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ƙasar INPPLC ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da hukumar tsaro ta DGSN da kuma hukumar shige da fice ta DGST.

An sanya hannu kan yarjejeniyoyin ne domin ƙarfafa samar da haɗin kai tsakanin muhimman hukumomi bayan jerin zanga-zangar da matasa suka jagoranta ta neman tsage gaskiya da gyara lamura a ƙasar.

Kazalika yarjejeniyar za ta samar da wani gurbi na bayar da horo na musamman ga hukumomi domin samar da ƙwarewa da kuma ƙarfafa ƙarfin gwamnati wajen tunkarar haɗuran cin hanci da rashawa.

Gwamnatin ta ce yarjejeniyar ta “nuna jajircewar Maroko wajen ƙarfafa hukumominta na cikin gida wajen yaƙi da cin hanci da rashawa ta wani tsari na haɗaka.”

Matakin yana zuwa ne bayan zanga-zanga a faɗin ƙasar da matasan da ake kira “Generation Z 212” suka shirya, wadda ta yi kira da yi gyara a fannin ilimi da lafiya da yaƙi da cin hanci da rashawa. Matasan sun dakatar da jerin zanga-zangar har zuwa ranar 9 ga watan Oktoba.

 

Rumbun Labarai
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan