| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Dakarun RSF sun kai hari kan wani masallaci da 'yan gudun hijira ke samun mafaka, mutum 13 sun rasu
Wani wanda ya shaida lamarin ya ce kusan mutum 70 ne ke samun mafaka a cikin masallacin bayan dakarun na RSF sun shiga gidajensu.
Dakarun RSF sun kai hari kan wani masallaci da 'yan gudun hijira ke samun mafaka, mutum 13 sun rasu
Dakarun RSF
9 Oktoba 2025

Harin makaman atilari da dakarun RSF na Sudan suka kai ya yi sanadin mutuwar mutum 13 a cikin wani masallaci a birnin El-Fasher da ke cikin mawuyacin hali, kamar yadda shaidu biyu suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Alhamis.

“Bayan harin da aka kai da rana, mun ciro gawawwaki 13 daga ƙaƙashin baraguzan ginin kuma muka binne su,” kamar yadda wani mazaunin yankin ya yi bayani game da harin da aka kai a ranar Laraba.

Wani wanda ya tsira daga harin ya ce: “Mun kasance iyalai 70 a cikin masallacin bayan ‘yan RSF sun shiga gidajenmu. Jiya, harsasai na makaman atilari sun rinƙa faɗowa, inda suka kashe mutane 13 daga cikinmu, suka raunata 20, kuma suka lalata wani ɓangare na masallacin.”

Harin ya zo ne kwana guda bayan sojojin Sudan sun bayyana cewa sun ƙwace wurare da dama da dakarun RSF ɗin ke rike da su a El-Fasher.

Ƙawanyar RSF

Sojojin sun kama wasu motocin yaƙi da dama, ba tare da bayar da adadi ba, kuma sun lalata guda shida, ciki har da motoci masu sulke, kamar yadda sojojin suka bayyana.

RSF ta yi wa El-Fasher ƙawanya tun daga ranar 10 ga Mayun 2024, duk da gargaɗin ƙasashen duniya game da haɗarin da ke fuskantar garin, wanda ke zama cibiyar ayyukan jin kai a jihohin biyar na Darfur.

A cikin watannin baya-bayan nan, yankunan da RSF ke iko da su sun ragu sosai a faɗin Sudan yayin da sojojin suka faɗaɗa nasarorin su na soja zuwa jihohin Khartoum, White Nile, da Kordofan ta Arewa.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher