| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Jirgi maras matuƙi na RSF ya kashe mutum 30 birnin Al-Fasher na Sudan
Kwamitin 'yan gwagwarmaya na Al-Fasher ya ce jirgin na RSF ya kai harin ne a sansanin 'yan gudun hijira na Dar al-Arqam da ke cikin harabar wata jami'a inda aƙalla mutum 30 suka rasu.
Jirgi maras matuƙi na RSF ya kashe mutum 30 birnin Al-Fasher na Sudan
Masu fafutuka sun ce birnin ya zama wurin da “gawawwaki suke jibge a fili" waɗanda na farar-hula ne masu fama da yunwa.
11 Oktoba 2025

Wani hari da jirgin sama mara matuki ya kashe akalla mutum 30 a wani sansanin 'yan gudun hijira a birnin Al-Fasher da ke yammacin Sudan a ranar Asabar, kamar yadda wata kungiyar masu fafutuka ta bayyana.

Kwamitin gwagwarmaya na Al-Fasher ya ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai hari a sansanin 'yan gudun hijira na Dar al-Arqam da ke cikin harabar wata jami'a.

Kwamitin ya bayyana cewa gawawwaki sun makale a cikin ramin karkashin kasa, yana mai bayyana lamarin a matsayin "kisan kiyashi" tare da yin kira ga al'ummar duniya su shiga tsakani.

Kwamitocin gwagwarmaya na yankin su ne masu fafutuka da ke hada kai wajen bayar da agaji da kuma rubuta rahotanni kan munanan abubuwan da ke faruwa a rikicin Sudan.

‘Gawawwaki jibge a fili’

RSF tana cikin yaki da sojojin gwamnatin Sudan tun watan Afrilu na 2023. Wannan rikici ya kashe dubban mutane, ya raba miliyoyi da muhallansu, kuma ya jefa kusan mutum miliyan 25 cikin yunwa mai tsanani.

Al-Fasher shi ne babban birnin jiha ta karshe a yankin Darfur mai fadi da ya ki fadawa hannun RSF, ya zama sabon filin yaki mai muhimmanci yayin da dakarun RSF ke kokarin karfafa ikon su a yammacin kasar.

Masu fafutuka sun ce birnin ya zama wurin da “gawawwaki suke jibge a fili" waɗanda na farar-hula ne masu fama da yunwa.

Kusan watanni 18 bayan fara yi a birnin Al-Fasher ƙawanya da RSF ta yi, birnin - wanda ke ɗauke da mutum 400,000 waɗanda suka maƙale - kusan komai ya soma ƙarewa.

An rufe wuraren sayar da miya

Abincin dabbobi da iyalai suka dogara da shi tsawon watanni ya yi karanci kuma yanzu ana sayar da shi a kan daruruwan daloli kowace jaka.

Yawancin gidajen abinci na birnin sun rufe saboda rashin abinci, kamar yadda kwamitocin gwagwarmaya na yankin suka bayyana.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher