| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Burkina Faso ta ƙi karɓar mutanen da aka kora daga Amurka
Matakin na Burkina Faso ya zo ne a daidai lokacin da ofishin jakadancin Amurka da ke Ouagadougou babban birnin ƙasar ya dakatar da ayyukan biza, matakin da gwamnatin Traore ta kira ''bita-da-ƙulli''.
Burkina Faso ta ƙi karɓar mutanen da aka kora daga Amurka
Shugaban kasar Burkina Faso Ibrahim Taore
10 Oktoba 2025

Burkina Faso ta ki ƙarɓar mutanen da aka kora daga Amurka, a wani mataki na watsi da ɗaya daga cikin manufofin Shugaba Donald Trump kan baƙin-haure.

Tun bayan komawar Trump Fadar White House, gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen tura mutane zuwa ƙasashe marasa karfi, musamman ƙasashen da ba su da alaka da su, a wani ɓangare na ƙoƙarin yaki da baƙin-haure.

A cikin ‘yan kwanakin nan a Afirka, ƙasar Eswatini da Ghana da Rwanda da kuma Sudan ta Kudu duk sun amince da mutanen da aka kora daga Amurka.

Sai dai kuma da yammacin ranar Alhamis, Ministan Harkokin Wajen Burkina Faso ya bayyana cewa, ƙasarsa da ke yankin yammacin Afirka ta yi watsi da matakin da Washington ta ɗauka.

"Bisa ƙa'ida, wannan shawara da muka ɗauka ba ta dace ba a wancan lokacin, sannan ta saɓawa ƙa'idar mutunci na ɗan’adam," kamar yadda Karamoko Jean-Marie Traore ya bayyana ta gidan talabijin din.

Masu AlakaTRT Afrika - Ghana za ta karɓi ƙarin mutum 40 da za a kora daga Amurka

Martanin Amurka

Kafin matakin na Burkina Faso, ofishin jakadancin Amurka da ke Ouagadougou babban birnin ƙasar, ya sanar da dakatar da ayyukansa na ba da biza ga galibin mutanen da ke zaune a Burkina Faso.

A maimakon haka, a yanzu 'yan ƙasar za su samu biyan buƙata ne a Lome, babban birnin makwabciyar ƙasar Togo.

"Shin wannan wata hanya ce ta matsin lamba a garemu? Ko kuma bita-da-ƙulli ne? To ko ma mene ne ... Burkina Faso ƙasa ce mai daraja, kuma wurin zuwa, ba wurin koro mutane ba ne," in ji Karamoko Jean-Marie Traore.

Tun bayan karɓar mulki a shekarar 2022 shugaban ƙasar Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traore, ya ɗaura ɗamarar ƙarfafa kyamar mulkin mallaka, tare da yin watsi da tsohuwar uwargijiyar ƙasar da ta yi mata mulkin mallaka wato Faransa da sauran kasashen yammacin duniya.

Rumbun Labarai
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu