| hausa
GABAS TA TSAKIYA
1 minti karatu
Isra'ila ta kashe fararen-hula 114 a Lebanon bayan saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta: MDD
Mai magana da yawun ofishin kare haƙƙin ɗan’adam na MDD ya ce ofishin na bibiyar farmakin jiragen sama na Isra'ila a kan gine-gine a ƙauyukan da ke kudu, ya kuma ce mutuwar fararen-hula ta ci gaba da ƙaruwa tun lokacin da aka tsagaita wuta.
Isra'ila ta kashe fararen-hula 114 a Lebanon bayan saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta: MDD
MDD ta ce an kashe fararen hula 114 a Lebanon.
13 Nuwamba 2025

Ofishin kare haƙƙin ɗan’adam na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta ta Nuwamba 2024 da Isra'ila ta yi a Lebanon ya haifar da mutuwar fararen-hula 114.

Mai magana da yawun ofishin, Thameen Al-Kheetan, ya bayyana wa Anadolu cewa ofishin na bibiyar farmakin jiragen sama na Isra'ila a kan gine-gine a ƙauyukan da ke kudu, ya kuma ce mutuwar fararen-hula ta ci gaba da ƙaruwa tun lokacin da aka tsagaita wuta.

Ya jaddada cewa dole ne a dakatar da kisan da ake ci gaba da yi wa fararen-hula "nan take", yana mai cewa mazauna yankin sun yi rayuwa cikin rashin tabbas da fargaba fiye da shekaru biyu.

Haka kuma ya yi kira da a gaggauta bin yarjejeniyar dakatar da tashin hankali da kuma dokokin jinƙai na kasa da kasa.

Sojojin Isra'ila sun kashe fiye da mutum 4,000 kuma sun jikkata kusan 17,000 a hare-harensu kan Lebanon, wanda suka fara kaiwa tun Oktoban 2023 inda zuwa Satumban 2024 hare-haren suka ƙazanta.

Rumbun Labarai
Afirka ta Kudu ta bai wa Falaɗinawa 'yan gudun hijira 150 izinin shiga ƙasarta
Mayakan Houthi sun ba da alamar dakatar da kai har kan Isra'ila da jiragen ruwa a Tekun Maliya
Israila ta rushe gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da sabon hari a Khan Younis
Trump ya ce “nan ba da jimawa ba” za a samar da dakarun tsaro na ƙasa da ƙasa a Gaza
Sau 27 Yahudawa 'yan-kama-wuri-zauna suka kutsa Masallacin Kudus a watan da ya wuce - Falasdinu
Bayanai na hukuma sun nuna cewa sojojin Isra'ila sun yi yunkurin kashe kansu sau 279 cikin wata 18
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta