| hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Kungiyar gwagwarmayar Hamas ta samu sahhalewar Shugaban Amurka Donald Trump kan ta ci gaba da aikin kula da tsaron cikin gida "don dakatar da matsalar".
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
13 Oktoba 2025

Dakarun ƙungiyar gwagwarmayar Falasɗinu Hamas sun kashe mutum 32 daga cikin wani “gungu” a birnin Gaza a wani yunƙurin tsaro da aka fara bayan yarjejeniyar tsagaita wuta da ta fara aiki a ranar Jumma’a.

Mutane shida daga cikin ‘yan ƙungiyar ta Hamas su ma sun rasa rayukansu a rikicin, kamar yadda wata majiyar tsaro ta Falasɗinu ta shaida wa Reuters a ranar Litinin.

Jami’in ya bayyana cewa aikin tsaron da aka gudanar a birnin Gaza an yi shi ne da nufin daƙile ayyukan mambobin wata “ƙungiya mai haɗari da ke da alaƙa da wani iyali a birnin Gaza”.

Wannan aiki ya kai ga kama mutum 24 tare da raunata wasu 30, in ji jami’in.

A baya, an ruwaito cewa Isra’ila ta tallafa wa wata ƙungiya mai ɗauke da makamai a Gaza da nufin raunana ikon Hamas a yankin na Falasɗinu. Ƙungiyar tana da hannu a wajen satar kayan agaji.

Tun bayan da yarjejeniyar tsagaita wuta a yaƙin Isra’ila a Gaza da ya shafe shekaru biyu ta fara aiki, Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta Gaza ta tura jami’an tsaro domin cike wani giɓi na tsaro da zai iya haifar da rashin doka da oda da kuma sata.

Yayin da Shugaban Amurka Donald Trump ya buƙaci Hamas ta ajiye makamai a wani shiri na kawo ƙarshen yakin Gaza, ya ba da dama ga Hamas ta gudanar da ayyukan tsaro na cikin gida, yana mai cewa suna son “dakatar da matsalolin” kuma “mun ba su izini zuwa wani lokaci.”

Hamas ta taɓa zargin Yasser Abu Shabab, shugaban wata ƙungiya, da magoya bayansa da yin haɗin baki da Isra’ila.

Jami’in tsaron na Hamas ya ce an “kashe” wani babban mataimaki na Abu Shabab tun bayan da aka fara wannan aikin tsaro tare bayan tsagaita wuta, kuma ya ce ana ci gaba da neman Abu Shabab.

“Aikin tsaron yana ci gaba kuma yana faɗaɗa har sai an gama shi gaba ɗaya, kuma ba za a bari kowace ƙungiya ta karya doka ba,” in ji shi.

Rumbun Labarai
Bayanai na hukuma sun nuna cewa sojojin Isra'ila sun yi yunkurin kashe kansu sau 279 cikin wata 18
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta
Wani bidiyo ya nuna yadda Isra'ila ke cin zarafin fursunonin Falasɗinawa gabanin sakin su
Trump, Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a birnin Sharm el-Sheikh a ranar Litinin
Sojojin Amurka sun isa Isra'ila domin sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Sojojin Isra'ila sun fara janyewa a hankali zuwa gabashin Gaza: Kafofin watsa labarai
Gwamnatin Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta Trump
Shekaru biyu na kisan kiyashin Isra'ila a Gaza: Falasdinawa suna shan yunwa da cin-amana