| hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Harin Isra'ila ya kashe mutum uku a Gaza bayan shafe dare ana ruwan bama-bamai duk da tsagaita wuta
Hukumar Tsaron Al'umma ta Falasɗinu a Gaza ta ce an zaƙulo mutum 3 daga iyalai biyu a cikin ɓaraguzai, sannan an jikkata aƙalla wasu mutane 15 a Khan Younis, a kudancin Gaza.
Harin Isra'ila ya kashe mutum uku a Gaza bayan shafe dare ana ruwan bama-bamai duk da tsagaita wuta
Isra'ila ta kashe Falasdinawa 280 kuma ta raunata 672 tun daga 11 ga Oktoba, a cewar sanarwar ranar Laraba daga Ma'aikatar Lafiya ta Gaza.
20 Nuwamba 2025

Hukumar Kula da Fararen Hula ta Falasɗinu a Gaza ta ce, a safiyar Alhamis an kashe Falasdinawa uku, wasu kuma sun ji rauni a wani harin jiragen sama na Isra'ila da aka kai kan wani gida a kudancin Gaza, abin da ke zama wata sabuwar keta yarjejeniyar tsagaita wuta ta 10 ga Oktoba.

Hukumar ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa tawagarta ta ciro gawawwaki uku da aƙalla mutane 15 da suka ji raunuka daga iyalai biyu bayan harin da aka kai wani gida a Bani Suheila, gabashin Khan Younis a kudancin Gaza.

A ranar Laraba, Ma'aikatar Lafiya a Gaza ta ba da rahoton cewa rundunar sojin Isra'ila ta kashe Falasɗinawa 25 kuma ta raunata 77 a jerin hare-hare kan wasu yankuna da Isra'ila ta riga ta janye daga cikinsu, abin da hukumomin Falasɗinawa suka ce keta yarjejeniyar tsagaita wuta ce.

Ma'aikatar ba ta fitar da ƙarin bayani kan wuraren da aka kai hari ko ainihin sunayen wadanda abin ya shafa ba.

Keta yarjejeniyar tsagaita wuta

Rundunar soja ta Isra'ila ta ce an kai harin ne a matsayin martani ga harbin bindiga da aka yi wa sojojinsu a Rafah, a kudancin Gaza.

Bayanan da ɓangarorin Falasɗinu da kungiyoyin kare hakkin ɗan adam, da hukumomin gwamnati suka tattara suna nuna cewa Isra'ila ta aikata ɗaruruwan keta yarjejeniyar tsagaita wuta tun bayan da aka fara aiwatar da ita a ranar 10 ga Oktoba.

Tun daga 11 ga Oktoba, Isra'ila ta kashe Falasɗinawa 280, sannan ta raunata 672, a cewar wata sanarwa da Ma'aikatar Lafiya ta Gaza ta fitar a ranar Laraba.

Tun daga farkon yaƙin ƙare-dangi da Isra'ila ta fara a Gaza a watan Oktoba 2023, rundunar sojan Isra'ila ta kashe kusan Falasɗinawa 70,000, mafi yawansu mata da yara, ta raunata sama da 170,000, ta kuma mayar da mafi yawan yankin zuwa ɓaraguzai.

Rumbun Labarai
Kotun Bangladesh ta yanke wa Sheikh Hasina hukuncin kisa
Koriya ta Kudu ta nemi yin tattaunawar soji da Koriya ta Arewa don kaucewa rikicin kan iyaka
Trump ya sayi takardun lamuni na aƙalla dala miliyan 82 tun daga Agustan 2025 – Bayanai
Trump ya bayar da umarnin haramta wa masu ƙiba shiga Amurka
Fadan 'yan daba da gwamnati ya jawo asarar rayuka 1,200 a cikin wata uku a Haiti - MDD
Numfashi na mana wahala saboda gurbacewar iska a birnin New Delhi na India
An soke tashin jiragen sama fiye da 2,000 a Amurka yayin da harkokin gwamnati ke ci gaba da dagulewa
Zinarin da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ke shigarwa ƙasarta daga Sudan ya ƙaru yayin da ake yaƙi
COP30: Manyan masu gurbata muhalli na duniya ba su je taron sauyin yanayi na Brazil ba
Rasha ta ce tana sa ido kan Nijeriya bayan barazanar da Trump ya yi ta kai hari kasar
Zohran Mamdani: Matashi Musulmi na farko ya lashe zaɓen Magajin Birnin New York
Yadda amfani da magungunan antibiotic barkatai ya sa cututtuka suka zama makamai
Rundunar Sojin Ruwan Pakistan ta kama mugwayen ƙwayoyi na dala biliyan ɗaya a Tekun Arebiya
An gano sauro a karon farko a ƙasar Iceland
Yadda hukumomi a India suke farautar Musulmai da suke cewa 'Ina son Annabi Muhammad'
Putin ya gargaɗi Trump cewa bai wa Ukraine makamai mai linzamin Tomahawk zai jawo matsala tsakaninsu
Abin da muka sani game da mummunar arangamar kan iyaka tsakanin sojin Pakistan da Afganistan
Waiwayen 1903: An taɓa yi wa Yahudawa tayin Afirka, kamar yadda ake so a mayar da Falasɗinawa yanzu
An naɗa Sarah Mullally mace ta farko Shugabar Cocin Ingila
Yadda mutuwar ɓauna a turmutsutsu ke sauya salon farautar manyan namun dawa