| Hausa
WASANNI
2 minti karatu
Yadda Tanzania ta tsallaka gaba da maki biyu kacal a gasar AFCON 2025
Tamkar almara, tawagar "Taifa Stars" ta Tanzania ta tsallaka zagayen 'yan-16 duk da cewa maki biyu kacal ta samu a Rukunin C, inda a yanzu za fuskanci Maroko mai masaukin baƙi.
Yadda Tanzania ta tsallaka gaba da maki biyu kacal a gasar AFCON 2025
Tanzania fans react after the match. / Reuters
31 Disamba 2025

A wani abu mai kama da almara da a gasar kofin ƙasashen Afirka ta AFCON 2025 da ake a Maroko, Tanzania ta samu cancantar zuwa zagayen siri-ɗaya-ƙwale, mai ƙasashe 16.

Wannan ne karo na farko da tawagar Tanzania da ake wa laƙabi da “Taifa Stars” ta samu damar kaiwa matakin gaba da na rukuni, tun bayan fara zuwanta gasar shekaru 45 da suka wuce.

A Rukunin C, Tanzania ta ƙare wasan ƙarshe tana matsayi na uku a bayan Nijeriya mai maki 9, wadda ke kan gaba, da kuma Tunisia mai maki 4 da ke matsayi na biyu.

A wasansu na farko, Tanzania ta sha kaye a hannun Nijeriya, sai kuma suka yi canjaras da Uganda da kuma Tunisia, inda suka ƙare da maki 2 kacal.

Kenan Tanzania ba ta yi nasarar cin ko da wasa guda ba. Hasali ma ta yi rashin nasara a wasa ɗaya, saɓanin Mali, wadda ta yi canjaras a duka wasanninta uku, amma ta zo ta biyu a Rukunin A da maki 3.

Fifiko kan Angola

Ko da cewa ba su ci ko wasa ɗaya ba, kuma sun samu maki biyu ne kacal, tawagar ta samu zarcewa zagayen gaba saboda zamowa cikin ƙasashe huɗu masu zarra da suka zo na uku a rukuninsu.

Wani abin lura shi ne Tanzania ta kammala zagayen rukuni da maki iri ɗaya da na Angola, wadda ke ta uku a Rukunin B, wato maki biyu amma ta gaza tsallakewa. Amma bambanci a yawan cin ƙwallo ne ya bai wa Tanzania fifiko.

Ɗanwasan Tanzania, Feisal Salum ya zama jarumi a idon magoya bayan ƙasar, bayan ƙwallon da ya ci Tunisia a minti na 48 wadda ta taimaka musu wafto maki ɗaya daga wasan.

Wannan wata babbar nasara ce ga Tanzania, wadda ke halartar gasar AFCON a karo na huɗu, inda a karon farko ta haura matakin rukuni.

Wani ƙarin abin alfahari ga ‘yan Tanzania shi ne suna cikin ƙasashen da za su karɓi baƙuncin gasar AFCON mai zuwa a shekarar 2027, tare da Kenya da Uganda.

Rumbun Labarai
Kwana 500 babu aski: Yadda sumar Frank Ilett ta zama shaidar matsalar Man United
Toni Kroos ya soki gasar ƙwallo ta Saudiyya game da raina tasirin Ronaldo
Victor Osimhen ya ci ƙwallo ta 200 a rayuwarsa ta wasa
Atletico Madrid ta ce ta cim ma yarjejeniya da Atalanta kan ɗanwasan gaban Nijeriya Ademola Lookman
Real Madrid za ta sake karawa da Benfica a wasan cike gurbi na Gasar Zakarun Turai
Mourinho ya bai wa Kocin Real Madrid haƙuri bayan Benfica ta doke Madrid a Gasar Zakarun Turai
CAF ta dakatar da kocin Senegal da Achraf Hakimi
Cole Palmer na son komawa Man United, Liverpool ba za ta rabu da kyaftin dinta, Virgil van Dijk ba
'Yanwasan Senegal sun samu kyautar kuɗi da fuloti saboda lashe Kofin AFCON
Dubban mutane sun halarci bikin karrama Zakarun Kofin AFCON a Senegal
Real Madrid ta sallami Xabi Alonso, ta nada Alvaro Arbeloa sabon koci
Hukumar CAF ta yi tir da rashin ɗa'a a zagayen kwata-fainal na AFCON 2025
Ɗan wasan Ghana Semenyo ya koma Man City daga Bournemouth kan dala miliyan 87
Yadda ƙarin kuɗaɗen tallafi ke taimaka wa mata ‘yanwasan ƙwallon ƙafa da ke fama da nakasa a Kenya
Wane ne Liam Rosenior, sabon kocin Chelsea?
Manchester United ta kori kocinta Ruben Amorim bayan ya soki shugabancin kungiyar
An sallami Anthony Joshua daga asibiti
Abubuwa 5 game da mai jiran Man United ta ci wasa 5 a jere, wanda ya kwana 452 ba aski
Hatsarin mota ya rutsa da Anthony Joshua a jihar Ogun ta Nijeriya
AFCON 2025: Za a fara wasannin ƙarshe na matakin rukuni don tantance ƙasashe 16 masu tsallakawa gaba