| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Gwamnatin Kebbi ta bayar da umarnin rufe duka makarantun gwamnati da na kuɗi a jihar
Wannan na zuwa ne bayan sace ɗalibai mata 25 daga wata makaranta da ke Maga.
Gwamnatin Kebbi ta bayar da umarnin rufe duka makarantun gwamnati da na kuɗi a jihar
Makarantar da kawai ba ta cikin jerin waɗanda aka rufe ita ce Kwalejin Kiwon Lafiya da Ungozoma da ke Birnin Kebbi, babban birnin jihar.
23 Nuwamba 2025

Gwamnatin Jihar Kebbi ta umarci rufe dukkan makarantun sakandare na gwamnati da na kuɗi tare da dukkan manyan makarantun gaba da sakandare a faɗin jihar.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da Kwamishinan Ilimi na Gaba da Sakandare Alhaji Issa Abubakar-Tunga da Kwamishinar Ilimi ta Firamare da Sakandare, Dakta Halima Bande, a Birnin Kebbi.

Kwamishinonin sun bayyana cewa rufe makarantun gwamnati da na kuɗi a jiha ya zama dole sakamakon hare-haren da aka kai a wasu sassan jihar kwanan nan.

Sun lissafa makarantun gaba da sakandare da abin ya shafa kamar haka:
Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kebbi da ke Dakingari da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Abdullahi Fodio da ke Aliero da Kwalejin Kimiyyar Lafiya da Fasaha ta Jega da Kwalejin Ilimi ta Adamu Augie da ke Argungu da Makarantar Sharar Fagen Shiga Jami’a ta Yauri.

Sai dai sun ce makarantar da kawai ba ta cikin jerin waɗanda aka rufe ita ce Kwalejin Kiwon Lafiya da Ungozoma da ke Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

Yayin da suke kira ga dukkan shugabannin makarantun da su bi umarnin gwamnati, kwamishinonin sun shawarce su da su kasance cikin natsuwa domin za a sanar da sabuwar ranar koma makarantun nan gaba.

Wannan na faruwa ne bayan sace dalibai mata 25 daga wata makaranta da ke Maga.

 

Rumbun Labarai
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?