| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Yaƙin Sudan: Fiye da yara 20 sun mutu sakamakon tsananin rashin abinci a cikin wata guda
Mutuwar yara 23 a yankin Kordofan ta nuna yadda ake da matuƙar buƙatar kayan jinƙai a ƙasar da ke arewa maso gabashin Afirka, inda yunwa ke ƙaruwa bayan fiye da watanni 30 na yaki.
Yaƙin Sudan: Fiye da yara 20 sun mutu sakamakon tsananin rashin abinci a cikin wata guda
An shafe fiye watanni 30 ana yaƙi a Sudan.
22 Nuwamba 2025

Fiye da yara ashirin sun mutu saboda matsalolin ƙarancin abinci a cikin wata guda a tsakiyar Sudan, inda rikici mai ƙarfi tsakanin sojojin ƙasar da rundunar RSF ke ci gaba da tayar da hankali, in ji wata ƙungiyar lafiya.

Mutuwar yara 23 a yankin Kordofan ta nuna yadda ake da matuƙar buƙatar kayan jinƙai a ƙasar da ke arewa maso gabashin Afirka, inda yunwa ke ƙaruwa bayan fiye da watanni 30 na yaki.

Sudan ta faɗa cikin ruɗani a watan Afrilun 2023 lokacin da rikicin neman iko tsakanin sojoji da rundunar Rapid Support Forces (RSF) ya ƙara ƙazancewa a babban birnin Khartoum da sauran sassan ƙasar.

A cewar ƙididdigar Majalisar Ɗinkin Duniya, yaƙin ya kashe fiye da mutane 40,000, amma ƙungiyoyin agaji suna cewa wannan adadin ya zarta haka inda ta ce akwai yiwuwar adadin ya wuce haka sosai.

A cewar ƙwararrun masu nazarin yunwa na duniya, zuwa watan Satumba an jefa kusan mutum 370,000 cikin yunwa a Kordofan da yammacin Sudan zuwa Satumba yayin da wasu miliyan 3.6 ke dab da faɗawa cikin tsananin yunwa, kamar yadda ƙwararrun suka bayyana.

Sudan Doctors Network, ƙungiyar kwararru da ke bibiyar rikicin, ta ce an ruwaito mutuwar yaran tsakanin 20 ga Oktoba da 20 ga Nuwamba a garin Kadugli da garuruwan Dilling da aka yi wa ƙawanya

A ranar Juma’a, ƙungiyar ta ce mutuwar ta kasance "sakamakon tsananin rashin abinci da ƙarancin kayayyakin masarufi" a wuraren biyu, inda takunkumi "ke hana shigowar abinci da magunguna kuma ke sanya rayukan dubban fararen hula cikin haɗari."

Kadugli, babban birnin lardin Kordofan ta Kudu,shi ne inda aka bayyana yunwa a farkon wannan watan ta hanyar Integrated Food Security Phase Classification (tsarin tantance matakin tsaro na abinci).

RSF ta kewaye garin Kadugli tsawon watanni, tare da dubban mutane suna makale yayin da rundunar ke ƙoƙarin karɓar ƙarin yankuna daga hannun sojojin Sudan.

Fadan neman iko da Kordofan ya ƙara ƙarfi a farkon wannan shekara bayan sojoji sun tilasta RSF ta fice daga Khartoum.

Rumbun Labarai
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi