| hausa
AFIRKA
1 minti karatu
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Kafofin watsa labarai na cikin gida sun ce jirgin yana ɗauke da kimanin mutum 120, kuma daga cikinsu kimanin 50 kawai aka iya cetowa kawo yanzu.
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Safara ta ruwa ya zama ruwan dare a Kongo saboda galibin hanyoyi marasa wucewa.
20 Nuwamba 2025

Ana neman kusan mutane 70 bayan wani jirgin ruwa ya kife a wani kogi a lardin Kasai, a tsakiyar Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo, in ji kafofin watsa labarai na yankin a ranar Laraba.

Jirgin yana kan hanyarsa ta zuwa babban birnin kasar Kinshasa daga tashar Bena Dibele, da ke da nisan fiye da kilomita 800, lokacin da ya nutse a ranar Litinin a kogin Sankuru, sakamakon guguwa, a cewar gidan rediyon Majalisar Dinkin Duniya.

“Jirgin yana ɗauke da kimanin mutane 120. An ceto kimanin 50 zuwa yanzu, kuma ana ci gaba da ayyukan neman waɗanda ba a same su ba,” in ji wani jami’in yankin Francois Ahoka.

Ahoka ya bayyana ƙalubalen da ƙungiyoyin ceto suka fuskanta, kuma ya yi kira ga iyalai da su ci gaba da tuntuɓar hukumomin yankin don taimakawa wajen tantance waɗanda aka ceto da gawawwakin wadanda suka mutu.

Ana yawan amfani da hanyoyin sufurin ruwa a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo saboda mafi yawan titunan ƙasar ba su da kyau.

Rumbun Labarai
Ghana za ta tura injiniyoyin soji don taimakawa wajen sake gina Jamaica bayan afkuwar guguwa
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi