| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
China ta gargaɗi ‘yan kasarta su kauce wa hadarin zama bayin ma'adinai a Jamhuriyar Tsakiyar Afirka
Wata sanarwa da ofishin jakadancin kasar ya fitar ranar Alhamis, ya ce ‘yan China da suke harkar hakar ma’adinai a ƙasashen Afirka a ‘yan shekarun nan sun fuskanci matsalolin tsaro ko “sun fuskanci gagarumin hadari na tsaro.”
China ta gargaɗi ‘yan kasarta su kauce wa hadarin zama bayin ma'adinai a Jamhuriyar Tsakiyar Afirka
Wajen hakar ma'adinai
21 Nuwamba 2025

Ofishin jakadancin China a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ya gargaɗi ‘yan kasar da su kauce wa yin aiki a masana’antu masu tsananin haɗari, kamar wuraren haƙar zinari, yana cewa za su iya zama “bayin haƙar ma’adinai.”

A wata sanarwa da ofishin ya fitar a ranar Alhamis, ya ce ‘yan China da suke harkar haƙar ma’adinai a ƙasashen Afirka a ‘yan shekarun nan sun fuskanci matsalolin tsaro ko “sun fuskanci gagarumin haɗari na tsaro.”

Yayin da wasu daga cikinsu suka fuskanci asarar kuɗaɗe saboda tarar da aka ɗaura musu ko zuba jarin da ya durƙushe, wasu sun fuskanci barazanar cin zarafi, a cewar sanarwar, tana cewa an kwace wa wasu daga cikinsu takardu, inda aka mayar da su “bayin hakar ma’adinai.”

“Kungiyoyi masu adawa da gwamnati da ke ɗaukan makamai sun kai wa wasu hari an kashe su, wasu kuma faɗa tsakanin ɓangarorin gwamnati da ƙungiyoyi da dama ya rutsa da su, wasu kuma sun mutu saboda munanan cutuka kamar zazzabin cizon sauro,” a cewar sanarwar.

Ta kuma yi gargaɗin cewa an kashe wasu ko an jikkata su a haɗarorin mota “da aka tsara” ko “rataya” saboda saɓani da ya biyo bayan rikinci da wasu masu ruwa da tsaki.

“Kada ku je wuraren da suke da haɗari a wajen Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya don yin aiki, sannan ku kauce wa masana’antu masu haɗari kamar wuraren haƙar zinari,” a cewar sanarwar ta ofishin jakadancin, yana kiran waɗanda suka riga suka shiga su dakata nan take, sannan su kai kansu ofishin jakadancin.

Rumbun Labarai
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi