| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Ghana za ta tura injiniyoyin soji don taimakawa wajen sake gina Jamaica bayan afkuwar guguwa
Shugaba John Mahama ya yi kira ga dukkan ƙasashen Afirka su miƙa taimako ga Jamaica da Cuba.
Ghana za ta tura injiniyoyin soji don taimakawa wajen sake gina Jamaica bayan afkuwar guguwa
Mutane sun taru cikin ɓaraguzai bayan guguwar da aka yi wa laƙabi da Hurricane Melissa ta afka a Jamaica ranar 30 ga watan Oktoba.
20 Nuwamba 2025

Shugaban Ghana John Dramani Mahama ya yi shelar shirye-shiryen tura mambobin rudununar injiniyoyin sojin Ghana na runduna ta 48 zuwa Jamaica domin tallafa wa ƙoƙarin sake gina ƙasar bayan lalata ababuwan da guguwar Hurricane Melissa ta yi.

Shugaba Mahama, da yake magana ranar Laraba yayin bikin tunawa da taron fafatukar kare baƙaƙen fata na biyar karo na 80, ya ce rundunar da ta soji ta ƙunshi sojoji masu ƙarewa a harkar injiniya na soji da na farar hula za ta taimaka wajen gina gidaje na wucen gadi wa ‘yan Jamaica da suka rsa gidajensu.

“Daga cikin waɗanda suka fi ba da ƙarin gwiwa na kishin Afirka da Ghana, mun yanke shawarar haɗa abinci da sauran abubuwa domin mu tura su ga ‘yan’uwanmu a Jamaica da Cuba," kamar yadda Mahama ya sanar da mahalarta taron.

Ana tsammanin tawagar ta ƙunshi injiniyoyi da mesin da kafintoci da sauran masu ƙwarewa a fasaha, kamar yadda kamfanin dillancin labaran ƙasar ya ruwaito.

Tallafin Nahiya

Mahama ya kuma yi amfani damar taron wajen kira ga ƙasashen Afirka da su miƙa taimakonsu zuwa Jamaica da Cuba, waɗanda masifar guguwar ta shafa, musamman bayan an samu kira kai-tsaye daga Firaministan Jamaica Holness.

"Kuma saboda haka, idan za ka iya kira ga ‘yan’uwanmu ‘yan Afirka da su taimaka mana, yawan ta’adin da aka samu a Jamaica ya fi ƙarfin abin da za mu iya gyarawa mu kaɗai," kamar yadda Shugaba Mahama ya ambato Firaministan Jamaica Andrew Holness yana cewa.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Ghana ta ce ta riga ta bayyana wa Ƙungiyar Tarayyar Afirka lamarin, tana mai kira ga ƙasashe mambobin ƙungiyar su ba da gudnumawar abin da za su iya wajen taimakawa domin samar da muhalli na wucin gadi.

Guguwar Hurricane Melissa, ɗaya ce daga cikin guguwa mafi ƙarfi da aka taɓa samu a tarihi a Tekun Atilantika, ta yi ɗaɗɗaya da yankin yammacin Jamaica ranar 28 ga watan Oktoba inda ta dira a Gabashin Cuba kuma ta lalata gidaje da amfanin gona.

Firaministan Andrew Holness ya ce aƙalla mutum 50 sun mutu kuma ya kiyasta cewa darajar ababuwan da suka lalace sun kai dala biliyan shida zuwa biliyan bakwai.

Mahama ya ce Ghana ta riga ta tura wasu kayayyakin agaji zuwa Jamaica.

 

Rumbun Labarai
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi