| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Hukumar NDLEA ta kama mutum 230 a samame daban-daban a Kano
An kai samamen ne a maɓoyar fitattun masu safarar ƙwayoyi a yankuna kamar su Kofar Ruwa, Tashar Rami, Rijiyar Lemo, Kurna, Mil Tara da sauran wurare da dama inda aka ƙwato tabar wiwi da sholisho da miyagun ƙwayoyi da makamai.
Hukumar NDLEA ta kama mutum 230 a samame daban-daban a Kano
NDLEA ta kama miyagun ƙwayoyi da makamai a Kano
21 Nuwamba 2025

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Nijeriya (NDLEA) Reshen Jihar Kano ta ce ta kama mutane 230 da ake zargi tare da ƙwato adadi mai yawa na miyagun ƙwayoyi da makamai a lokacin wani samame na musamman na tsawon kwanaki 30 a da jami’an hukumar suka kai a faɗin Jihar Kano.

Kwamandan Tsare-Tsaren Hukumar, ACGN A.I. Ahmad ne ya bayyana haka yayin wani taron manema labarai a Kano, kamar yadda gidan rediyon Nijeriya ya ruwaito.

Ya ce an gudanar da samamen ne tare da hadin gwiwar Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya da Hukumar Tsaro ta Farar-Hula (NSCDC) da Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya da Hukumar Gyaran Hali ta Nijeriya.

Ahmad ya bayyana cewa an kai samamen ne a kan maɓoyar fitattun masu safarar ƙwayoyi a yankuna kamar su Kofar Ruwa, Tashar Rami, Rijiyar Lemo, Kurna, Mil Tara, Zage, Dorayi Karshen Waya, Dawanau, Filin Idi, Research, Rimi Market, Zango, Kofar Mata, Kano Line da Ladanai.

Ya ce a lokacin samamen, jami’an sun kwato tabar wiwi da sholisho maganin tari mai codeine, sannan da makamai da dama waɗanda aka ƙera a cikin gida.

A cewarsa, wannan samamen ya rage yawan shaye-shaye da laifuffukan da suka shafi miyagun kwayoyi, ciki har da ta’addanci na matasa da ƙwacen wayoyi, inda ya ƙara da cewa al’umma sun fara jin tasirin hakan.

Ahmad ya yaba da haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, yana mai cewa hadin gwiwar ya ƙarfafa zaman lafiya da tsaro a jihar.

Ya jinjina wa jagorancin Kwamishinan ‘Yan Sanda, CP Ibrahim Adamu Bakori, bisa yadda yake inganta hadin kai tsakanin hukumomi, tare da gode wa Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) kan rawar da ta taka ta hanyar bayanan sirri.

Haka kuma ya gode wa Gwamnatin Jihar Kano, ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa goyon bayanta wajen yaƙi da shaye-shaye da ta’addancin samari, yana mai cewa jajircewar gwamnati ta ƙarfafa ƙoƙarin tabbatar da tsaro da farfaɗo da masu fama da shaye-shaye.

Kwamandan ya yi kira ga shugabannin al’umma, iyaye, ƙungiyoyin farar-hula, da jama’a gaba ɗaya da su haɗa kai da hukumomin tsaro wajen yaƙi da shaye-shaye.

Rumbun Labarai
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?