| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
An ƙaddamar da taron shugabannin ƙasashen G20 a Afirka ta Kudu
A yayin wannan taron wanda jigonsa zai kasance 'hadin kai, daidaito da ɗorewa', shi ne taron G20 na farko da aka taba gudanarwa a nahiyar Afrika, kuma zai mayar da hankali kan sassauta bashi ga ƙasashe masu ƙaramin ƙarfi.
An ƙaddamar da taron shugabannin ƙasashen G20 a Afirka ta Kudu
Taron G20
22 Nuwamba 2025

An fara taron shugabannin ƙungiyar G20 a Johannesburg da ke Afrika ta Kudu, inda shugaban ƙasar Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa ya gabatar da jawabi na farko yayin da wakilai suka hallara don tattaunawa ta tsawon kwanaki biyu.

A yayin wannan taron wanda jigonsa zai kasance 'hadin kai, daidaito da ɗorewa', shi ne taron G20 na farko da aka taba gudanarwa a nahiyar Afrika, kuma zai mayar da hankali kan sassauta bashi ga ƙasashe masu ƙaramin ƙarfi — wata babbar matsala da ke hana ci gaba kasashen da ke tasowa.

Shugabannin za su kuma tattauna yadda za a samu daidaito kan sauyin yanayi da sauya zuwa hanyoyin samar da makamashi masu tsafta, tare da sauran muhimman manufofi.

Ajandar ta kunshi tattaunawa kan hadin kai na ciki da kuma hanyar dabarun kungiyar, yayin da aka shirya shugabannin su gudanar da jerin ganawa-biyu a gefe a lokacin wannan taron na kwanaki biyu.

Amurka ba za ta halarci taron G20 ba

Ministan Harkokin Wajen Afrika ta Kudu, Ronald Lamola, ya ce a wannan makon ana sa ran kasashe 42 za su halarci wannan taron na tarihi na G20 da kasar ke karɓar baƙunci.

Amurka, wacce ta kasance daya daga cikin kasashen da suka kafa G20, ta yi watsi da halartar taron bana.

A farkon wannan watan, Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar cewa ba zai aika jami'in Amurka zuwa Johannesburg don taron ba, inda ya zargi Afrika ta Kudu da 'tauye hakkin ɗan’adam kan al'ummar al’ummar ‘yan Afrikaana farar fata — ikirarin da gwamnatin Afrika ta Kudu ta musanta sau da yawa cewa ba su da tushe.

A wannan shekara, dangantaka tsakanin Washington da Pretoria ta kai mafi karancin mataki saboda bambance-bambance a kan manufofin waje da na cikin gida.

An kafa G20 a 1999, kuma ta kunshi kasashe 19 da kungiyoyi na yanki guda biyu — Tarayyar Turai (EU) da Kungiyar Tarayyar Afirka (AU).

Rumbun Labarai
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi